الأحد، 30 يونيو 2019

kuma abin da ya ke a gare ku na ni'ima to daga Allah ne


Hudubar Masllacin Annabi na shaikh Abdulbari Bin Awad Assubaiti 25/10/1440Ah 28/6/2019Ac
Ni'imomin Allah ga bayinSa suna da yawa ba za'a iya iyakance su ba,mai dunbin yawa ne da ba za a iya kwalkwale su ba, suna bibiyan juna basu karewa :Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Allah ne wanda ya halicci sammai da kasa, kuma ya saukar da ruwa daga sama sa'anan ya fitar game da shi daga 'ya'yan itace, arziki  domin ku, kuma ya hore jirgin ruwa yayi gudu a cikin teku da umarninSa, kuma ya hore muku koguna.kuma ya hore muku rana da wata suna madawwama biyu, kuma ya hore muku dare da wuni. Kuma ya baku dukkan abin da ku ka roke shi, kuma idan kun kidaya ni'imar Allah ba za ku lissafe ta ba, lalle ne mutum hakika mai yawan zalunci ne mai yawan kafurci ).
Samuwan abubuwa masu amfani da tunkude  cutarwa da ma dukkan alheri da bawa yake samu ni'ima ce daga Allah zuwa gare shi ; na ilimi da imani da aiki da zuriya da masauki da abin hawa da walwala da nasara Allah Madaukakin sarki ya ce (kuma abin da ya ke a gare ku na ni'ima to daga Allah ne) kuma lura da abin da ya ke kewaye da mu yana kaimu ga jin niimar Allah , Allah madaukakin sarki ya ce (To mutum ya duba zuwa ga abincinsa) kuma ya ce (To mutum ya duba daga me aka halicce shi).
Muminai na dubi ga ni'imar Allah na ciki da na waje: hakan sai ya kara musu imani ya kusanto da su ga Ubangijinsu suna masu ikirari da baiwarsa da alherinSa da falalarSa a gare su, Allah madukakin sarki ya ce : (suna yin gori gare ka don sun musulunta, kace kada ku yi gorin kun musulunta a kai na, Aa Allah ne ke yi muku gori domin ya shiryar da ku ga imani, idan kun kasance masu gaskiya.)
Mumini da kaifin hankalinsa da nunan tunaninsa; na dubi ga ni'imomin Allah da ke kewaye da shi, Allah madaukakin sarki ya ce yana mai sifanta halin muminin da zai karbi aikinsa : (Har a lokacin da ya kai ga mafi karfinsa,kuma ya kai shekara arba'in yace ya Ubangiji na! ka kange ni, domin in godewa ni'imarka, wadda ka ni'imta a kaina, da kuma a kan mahaifa na biyu, kuma domin in aikata aikin kwarai, wanda ka ke yarda da shi)
 Idan zuciyar bawa ta cika da imani; ni'ima ta godiya ga ni'imar sai ta tabbatu a gare shi, sai kai komonsa  su gyaru halayensa su tsarkaka,sai ya yi dace, Allah madaukakin sarki ya ce yana mai gori ga bayinSa: (kuma Allah ya soyar da imani a gare ku, kuma ya kawata shi a cikin zukatanku, kuma ya kyamatar da kafirci da fasikanci da sabo zuwa gare ku, wadannan sune shiryayyu. Bisa ga Falala daga Allah da ni'ima, kuma Allah Masani ne Mai hikima).

Ikirari da ni'imar Allah na daga cikin abin da ke hukunta tuna ni'imomin Allah, da kuma jingina su ga wanda ya bada su - daukaka ya tabbata a gare shi,- wanda ke dakon ni'imomi to ba zai gushe ba yana tuna mai bada su, wanda shi ne Allah Madaukaki  Mai ni'imtarwa da dukkan ni'imomi wadanda muke jujjuyawa a cikinta,
Yin ikirari da ni'imar Allah shine mabudin dukkan Alheri, zai sanya harshen mumini yana furta (Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai. Mai mulki ranar sakayya)  a tsawon wuninsa da darensa.
Idan musulmi ya tabbatar da ni'imar Allah a kan sa, ya yi ikirari da falolin UbangijinSa da ke kewaye da shi,; to lalle zai yi amfani da wadannan ni'imomin wurin neman yardar Allah Madaukaki, ga Annabi Sulaiman Amincin Allah ya tabbata a gare shi yana rokon UbangijinSa; (ya Ubangiji ka cusa mini in gode wa ni'imarka, wadda ka ni'imta ta a gare ni, da kuma ga mahaifana biyu, kuma in aikata aiki na kwarai, wanda kake yarda da shi, kuma ka shigar da ni sabo da rahamarka a cikin bayinka salihai,)
Ga Annabi musa abokin maganar Allah yana kulla alkawari ga Ubangijinsa     ; ( Yace Ya Ubangiji! Domin abin da ka ni'imta shi a kai na saboda haka ba zan kasance mai taimako ga masu laifi ba)
Idan musulmi ya tabbatar da ni'imar Allah a kan sa, to zai bayyana wadannan ni'imomin ne halin yana mai godiya da yabo, ba yana mai alfahari da girman kai ba, Allah madukakin sarki ya ce:    (kuma amma ni'imar Ubangijinka sai ka fada (domin godiya). Wato ka labarta wa mutane abin da Allah ya ma na ni'ima kana mai girmama wa ga Mai ni'imtarwan.
Ya zo a hadisi ( Idan Allah ya yi ni'ima ga bawa to yana so ya ga gurbin ni'iman a gare shi).Baihaki ya rawaito da isnadi hasan.
An karbo daga Abul Ahwas Aufu dan malik dan Nadlah daga Babansa yace :( Na zo ga Manzon Allah a halin ina wani yanayi na tufafi mara fasali, sai ya ce : kana da dukiya? Sai na ce :E, sai yace daga wani irin dukiya? Sai na ce : daga dukkan nau'i Allah ya bani; na daga rakuma da bayi da dabbobi, sai yace : To idan Allah ya baka dukiya ta aga hakan tare da kai).Ibnu Hibban ya rawaito a sahihinsa
  Idan ni'imomi sun tattaru ga rayuwar bawa ;to fa wani albishir ne na alheri ga ma'abocinsu muddin ya fahimci hakkinsu da ke kan shi kuma ya sauke wajibi, kuma ya sarrafa su ta hanyar da ke nuna godiya da bauta ga Allah.Amma wanda ya rudu da kansa ya yi jiji da kai da abin da Allah ya bashi na ni'ima har ma ya jinginta ta ga kansa kamar yadda Allah ya ambata a kur'ani bisa harshen Fir'auna yayin da ya ke cewa : (kuma Fir'auna ya yi kira a cikin mutanensa, yace : ya mutane na! ashe mulkin masar ba a gare ni yake ba? Kuma wadannan koguna suna gudana daga karkashi na? ashe ba ku gani ba)
 Haka ma Karuna yace( An bani shi akan wani ilimi wanda yake gare ni kawai)
To irin wannan ni'imar ce take juyawa azaba alherinta ya zama sharri samunta ya zama bala'i.
Mafi girman godiya ita ce gaggauta wa zuwa ga ibada Allah yace (A'a Allah kadai zaka bauta wa kuma kasance cikin masu godiya).
To kuma idan bawa ya yi kokari wurin bautawa Ubangijinsa yana mai godiya a gare shi bisa ni'imominsa, to lallai sakayyarsa a gurin Allah na daga cikin irin aikin da ya yi. Allah Madaukakin sarki ya ce : (Lalle wannan ya kasance sakayya a gare ku, lalle aikin ku ya kasance abin godewa).
Bawa ba zai iya sauke nauyin godiyan ni'immomi ba duk yadda ya yi kokari , ya isan mishi ya yi kokari ya samu yardan Allah Madaukaki! Ya samu ya yi godiya na gabadaya da godiya na musamman, a duk lokacin da ni'ima ta sake samuwa sai ya sake mata sabuwar godiya. Ya zo a hadisi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce (wanda ya ce idan ya wayi gari; Ya Allah abin da ya wayi gari da ni na ni'ima ko wani daga cikin halittunka to daga gareka ne yake kai kadanka baka da abokin tarayya kuma dukkan yabo da godiya naka ne to hakika ya sauke nauyin godiya na wannan rana, wanda ya ce idan ya yi yammaci Ya Allah duk abin da ya yi yammaci da ni na ni'ima ko daya daga cikin halittunka to daga gareka yake kai kadanka baka da abokin tarayya, to yabo da godiya ya tabbata agreka to hakika ya sauke nauyin godiya na wannan dare).
kuma  (An karbo daga Rifaa dan Rafi' Azzuraki ya ce mun kasance wata rana muna salla a bayan Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yin da ya daga kansa daga ruku'u kuma ya ce :Allah ya amsa ga wadanda suka gode mishi sai wani mutum a bayan shi ya ce:Ubangijinmu godiya ta tabbata gareka ,godiya mai yawa tsarkakakkiya mai albarka a cikinta yayinda Manzon Allah ya idar da sallah sai ya ce: wanene yayi magana dazu? sai wanan mutumi ya ce nine ya manzon Allah! sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce hakika naga mala'iku talatin da dori suna rige rige waye zai fara rubuta ta )Hakim ne ya rawaito da ibnu hibba da isnadi ingantacce
 Musulmi zai yi gaggawa zuwa kofan adu'a yana rokon Ubangijinsa da ya mishi ilhama na godiya, domin ya kankare tawaya da nakasa, ababin niimomi (kuma ka samu masu godiya bisa niimarka masu kuma kyawtata yabo da ita agare ka to ka karbe ta ka cikata agare mu )Ibnu Hibban ne ya rawaito.
Amma wanda idonsa ya makance daga ganin ni'imomin Allah to hakika wannan ya fada  rabon shaidan da waswasinsa da makircinsa, kura'ani ya hakaito hakan daga gare shi (saannan zan zo musu daga gaba garesu kuma daga baya garesu kuma daga damansu da kuma hagunsu ba za ka samu mafiya yawansu ba suna masu godiya)
Musulmi na gafala daga riskan ni'imomin Allah a gare shi yana mai   rainata ma a lokacin da ya ga abin da ke hanun wasu na ni'imomi. A cikin sahihu muslim daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(ku yi dubi zuwa ga na kasa da ku kar kuyi dubi zuwa ga wanda ya ke sama da ku domin haka ya fi dacewa don kar ku rena niimar Allah a gare ku.
Na daga cikin munanta ladabi ga  Allah dulmuya cikin ni'imomi da manta Mai yin ni'imar da kuma zurfafa wa cikin farin ciki da manta Mai yaye bakin ciki  da bacin rai, Allah Madaukakin sarki ya ce (kamar wancan ne Allah ya ke cika niimarsa a kanku tsammaninku kuna mika wuya )
(To idan sun juya to abin da ya wajaba a kanka shi ne isarwa bayyananniya) (suna sanin niimar Allah sa'annan kuma suna musantawa kuma mafi yawansu kafirai ne )kuma ya ce: (kuma wanda ya musanya niimar Allah bayan ta zo mishi to lalle ne Allah mai tsananin ukuba ne).
                 
                           Huduba ta biyu
 Mai hankali ya na kiyaye amfani da  ni'imomin Allah ba tare da ya yi sakaci da hakkin Allah a ciki ba  da bauta da godiya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Idan ka ga Allah yana baiwa bawa abin da ya ke so alhali shi kuma bawan yana saba mishi to lalle hakan a gareshi daurin talala ne sannan sai aka yayeta da wannan ayan(saannan kuma A lokacin da suka manta abin da aka tunatar da su da shi sai muka bude a kansu kofofin dukkan kome har a lokacin da suka yi farinciki da abin da aka basu, muka kama su kwasam, sai gasu sun yi tsuru- tsuru, sai aka katse karshen mutanen,wadan da suka yi zalunci, kuma godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai ) Ahmad da Baihaki ne suka rawaito Albani ya inganta shi.

Kuma musulmi na sanya bautarsa a hade da abin da ya ke riska na ni'ima, idan an bashi ni'ima sai ya yarda in an dauke sai ya yi fushi, to wannan sifa ce abin zargi,
 Allah Madaukakin sarki ya ce (kuma cikin mutane akwai mai bauta wa Allah bisa gefe, sa'annan idan wani alheri ya same shi sai ya natsu da shi, kuma idan wata fitina ta same shi sai ya juya baya akan fuskarsa ya yi hasarar duniya da lahira.
An karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah kara yarda a gare su, yace: (kuma cikin mutane akwai mai bauta wa Allah bisa gefe,) Mutum ne zai zo Madina idan matarsa ta haifi da dokin sa ya haihu sai ya ce : wannan Addini ne mai kyau, idan matarsa bata haihu ba dokin sa bai haihu ba sai ya ce : wannan mummunan addini ne).

الجمعة، 21 يونيو 2019

kofofin tuba


Hudubar Masllacin Annabi na 11-10 -1440AH/14-6-2019 AD na Sheikh Abdullah bin Abdurrahman Albu'aijan.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode masa muna neman taimakonsa muna neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi duk wanda ya batar da shi ba zaka sama mishi majibinci mai shiryarwa ba.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, ya halitta kuma ya daidaita abin halitta ya kaddara (abin da ya so) ya shiryar, na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma manzon sa ne, wanda ya turo shi da gaskiya da shiriya, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da duk wanda ya bi sawun shi,ya bi tafarkinsa da kyautatawa har zuwa ranar sakayya,
Bayan haka: Lallai mafi alherin zance shi ne littafin Allah, kuma mafi alherin shiryarwa shine shiryarwa Muhammad dan Abdullah, Mafi sharrin al'amura sune fararrunta, dukkan fararrun abubuwa bidiah ne, dukkan bidiah bata ne dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah … ku ji tsoron Allah cikin abin da ya umarta, ku hanu daga abin da ya hana ya tsawatar, ku sani dukkan karami da babba ana rubuta shi, (ya ku wadanda suka yi mani ku bi Allah da takawa, kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma ku bi Allah da takawa lalle Allah mai kididdigewa ne ga abin da ku ke aikatawa,)
Ya ku bayin bayin Allah!
Lokaci na albarka da falala da alheri da da'a ranakunsa ya kare an nade ayyukansa, lalle wata ne mai girman falala, tasirin sa a cikin Al'uma na da ban mamaki, masu nasara cikin shi sun ribata,masu kokari cikinsa sun samu ganima,ina ma da mun san wanda aka karbi ayyukansa mu mishi barka! Wane ne baa karba mishi ba mu jajanta mishi,
Madalla da farincikin wanda suka rabauta, Allah ya musu ilhamar tuba, ya datar da su ga biyayya, muna roka musu Allah da ya karba musu ya dora su kan daidai.
Ya  kaiton hasarar wadanda suka rasa wannan alheri aka katange  su daga Ubangijin su, damammaki a rayuwa suka kwace musu.ga lokutan alheri basu ribaci komai ba sai hasara da nadama,
Sai dai ya jama'ar musulmi ! kofofin tuba basu gushe ba suna bude ba a rufe su ba bayan watan ramadan,Ubangijinmu mabuwayi da daukaka yana karbar tuba daga bayin sa a kowane zamani da guri  (Shi ne yake karbar tuba daga bayin sa kuma yana yafe munana, kuma ya san abin da kuke aikatawa).
     Ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :Lalle Allah ya fi farinciki   da tuban bawansa mumini  akan mutumin da  yake cikin kasa ta sahara wacce  ke da ababan halakarwa   yana tare da dabbarsa  abin cin shi da abin shan sa na kanta   sai ya yi bacci , da ya farka sai ya ga ta tafi  ya yi ta nemanta  har sai da  kishi ya cimmasa  sai ya ce bari na koma wurina da na kasance a cikin shi  sai na je na yi bacci har ma na mutu  sai ya dora kanshi  a bisa damtsen shi don ya mutu yana halin haka  sai ga dabbarsa a kan sa  tare da ita ga guzurin shi da abin cin shi  da abin shan sa  sai  ya rike linzamin ta yayi kuskure don tsananin farin ciki yana mai cewa ya Allah kai ne bawana ni ne Ubangijin ka  .
An karbo daga Abu Huraira  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:(Idan wani yanki na dare ya shude ko kuma wani sulusin  shi , Ubangijin mu mai tsarki da daukaka zai sauko  zuwa ga  sama na  duniya  sai ya ce:-
Ko shin akwai mai tambaya na ba shi , ko shin akwai mai roko na amsa mishi , shin akwai mai neman gafara a gafarta masa har gari ya waye  . Muslim ne ya rawaito)
Zuwa ga wanda daman ramadan ya kwace mishi  to ka yi gaggawa zuwa ga tuba  kafin lokaci ya tsere   da kuma shammatan ajali kada ka yanke tsammani don duk dan adam mai kuskure ne  abin zargi  na ga wanda ya doge  kuma alhali yana da Ubangiji mai gafarta zunubai kuma bai nemi gafarar sa ba , ba don kun kasance kuna kusakurai ba kuma kuna neman gafara da  Allah ya tafiyar da ku ya kawo wasu mutane wadan da suna kuskure kuma suna neman gafara sai Allah ya gafarta musu .
YA KU BAYIN ALLAH:
Ku ji tsoron Allah kuma ku nemi gafarar sa  kuma ku koma zuwa gare shi ku mar da'a  kada ku jinkirta tuba domin  mutuwa na zuwa bagtatan  .
Allah madaukakin sarki ya ce :-(Ku tuba suwa ga Allah gaba dayanku ya ku muminai  ko za ku  rabauta)
Kuma ya ce :-( Ka ce  ya ku bayi na wadanda suka   barnatawa kawunan su  kada ku yanke tsammani daga rahamar Allah lallai Allah yana gafarta zunubai baki daya  lallai shi mai gafara ne kuma mai jin kai .  Ku koma zuwa  ga Ubangijinku  ku mika wuya gare shi  kafin azaba ya zo muku  sa'annan ba za a taimaka muku ba , ku bi mafi kyaun  abin da aka saukar gare ku daga Ubangijin ku  tun kafin azaba ya zo muku  bagtatan a halin kuna baku sani ba  kada rayi ta ce  ya hasara ta  bisa  abin da na yi sakaci a janibin Allah  , ko da na kasance cikin  wadan da suke masu isgili  ko kuma ta ce ina ma da Allah ya shirye ni  da na  kasance cikin masu takawa  , ko kuma ta ce ya yin da ta ga azaba  ina ma da ina da kome da na kasance cikin masu kyautatawa 

YA KU MUSULMAI:
Lallai ibada na da tasiri  cikin halayen ma'abocinta Allah madaukakin sarkiya ce :-(Lallai sallah na hani ga alfasha  da munkari)
Na daga cikin alamomin karban ayyuka  akwai canzawan halayen zuwa mafi kyan hali  a daya bangaren kuma  yana daga cikin alamomi na  rasa alheri da rashin karban aiki  akwai komawa baya  daga da'a  bayan shudewan ramadana  yanayin halaye ya canza zuwa mafi muni  domin sabo sashi na janyo sashi , madalla da kakkyawa bayan mummuna  sai ta goge ta  mafi kyaunta kuma shi ne kyakkyawa bayan kyakkyawa  tana mai binta , ku roki Allah tabbatuwa akan da'a har zuwa mutuwa  kuma ku nemi tsarin Allah  daga juyawar zukata  haka nan kuma daga warwarewa bayan daurewa .

 Abin mamaki da munin  kaskanci  na sabo  bayan izza ta da'a  tir da  talauci na  kwadayi bayan wadatuwa da wadatan zuci  ku roki Allah tabbatuwa , ya tabbata daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Lallai dayanku  zai yi aiki irin na 'yan aljanna  har sai ya kasance tsakanin shi da ita  face zira'I  sai littafin sa ya rigaya  , sai ya yi aiki irin na 'yan wuta sai ya shige ta ,  kuma lallai dayan ku zai yi aiki irin na 'yan wuta   har sai ya kasance tsakanin shi da ita face zira'I sai littafin shi ya rigaya sai ya shigeta  Buhari ne ya rawaito)
Ina fadin abin da kuke ji ……….

HADUBA TA BIYU

Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga Allah wanda  yake karban tuba daga bayin sa  kuma yake yafe kusakurai kuma ya san abin da kuke aikatawa ,  kuma yana amsa kiran wadan da suka yi imani kuma  suka yi aiki na kwarai   kuma yana kara musu daga falalar sa .
 YA KU MUSULMAI :
Watanni dukan su lokuta ne na ibada  ko da sun sha banban  sun saba a wurin fifiko  da ayyuka  rayuwa dukkanta   dama ce ta aiki  da biyayya   ko wanne yana wayan gari yana mai saida kan sa akwai mai 'yantata akwai kuma mai halakata ,  kuma kowa ana yassare mi shi abin da aka halicce shi  akanta   , .
To ku sabarwa kawunan da da'a ku nemi taimako game da ita da tuba  da neman gafara  da komawa zuwa gare shi da marairaicewa  da kuma murakaban Allah  guda mai rinjayi  a sirri kuma da bayyane a dare da wuni .
 (Ku bar  sabo na zahiri da na badinin  sa  lallai wadanda suke aikata laifi za a sakanya musu da abinda suka kasance suna aikatawa)
YA KU BAYIN ALLAH:
Ku rantawa Allah rance kyakkyawa , ku kaddamarwa kawunan ku abu mai amfani , (Duk wani abu da za ku kaddamar wa kawunan ku na alheri za ku same shi a wurin Allah).
(Wane ne zai rantawa Allah rance mai kyau sai ya ribanya mishi ribanyawa mai yawa).
Sannan ku sani cewa azumi garkuwa ne , dukkan aikin dan adam  na shi ne  sai azumi to shi na Allah ne zai sakanya game da shi , to duk wanda zai iya  a cikin ku ya azumci azumi shida a shauwal  to lallai hakan na daga cikin sunna  kuma aiki ne na musdafa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
An karbo dga Abu ayubal Ansari Allah ya kara yarda a gare shi ya ce  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbataa agare shi ya ce :-(Duk wanda ya yi azumin ramadana  sannan ya bi da guda shida  a shauwal  zai kasance kamar ya yi azumi na shekara ne )Muslim ne ya rawaito
Sabo da kyakkyawa guda na da lada goma kamarta,to ramadana na da ladan wata goma, guda shidan kuma ladan wata biyu, kuma adadin watanni a gurin Allah goma sha biyu ne,
Ba laifi mutum ya yi azumin a jere ko a rarrabe, muddin dai a cikin watan shauwal ne, tamkar tana matsayin sunnoni ne na ratibi game da sallolin farilla,tana cike gurbin tawaya ne da aka samu a farilla.

        YA KU MUSULMAI :
Ku ji tsoron Allah,iya iyawanku,ku yi riko da addininku,ku kankame sunnar Annabinku, ku kuma gyara tsakaninku,ku kiyaye hadin kanku, da garinku, ku zama hanu guda kan abokin gabanku, ku roki Allah da ya tabbatar da ku ya datar da ku,
Bayan haka YA KU MUSULMAI :
Lallai abin da masu ketare iyaka suka suka aikata na harbi kan 'yan kasa da mazauna, da tsorata amintattu, da zubar da jinin wanda bai ci ba bai sha ba.da yara da mata, da keta alfarman wurare masu tsarki manya da gari mai alfarma, na daga cikin manyan laifuka abin ki ga dukkan addinai, kuma yana cin karo da ginshikai na musulunci, Alla maida musu sharrinsu a kan su.ya sanya yakinsu a tsakaninsu, kuma ya yanke karshensu.
Ya Allah ka kare wannan kasa da kariyarka.