الخميس، 27 أبريل 2017

MIKA WUYA GA ALLAH

HUDUBAR JUMA'A TA MASALLACIN ANNABI  2 GA SHA'ABAN 1438 AH NA SHAIKH HUSAINI AL- ASSHAIK.
HUDUBAR FARKO
A LOKACIN DA DUNIYA KE KUSA TA ZAMA TA HADE GU GUDA SAKAMAKON BUNKASA NA ILIMI DA CI GABA DA DAN ADAM KE SAMU,SAI GA FANDAREWA NA MANHAJA NA YAWAITA DA FITINTINU MASU HADARI,WADANDA KE SHAFAR ADDINI  NA GASKIYA DA KYAWAWAN DABIU, HAKA NE DAN ADAM YAKE DA ZARAN YA SAMU WATA DAMA DON FADIN ALBARKACIN BAKINSA DA TUNANINSA DA MANHAJARSA.
KU SAURARA! LALLE MUSULMAI A YAU SUNA CIKIN BUKATAR LAFIYAYYEN MA'AUNI DA ZASU BANBANCE TSAKANIN ABU MAI INGANCI DA MARA KYAU, TO AI SUNA DA WASU TABBATATUN ABUBUWA DAGA UBANGIJI DA WA SU KA'IDOJI DAGA ALLAH WADANDA ZAI TSALLAKA DASU ZUWA BAKIN GABA NA TSIRA DAGA DUKKAN WATA FIKIRA MAI ILLA DA KUMA FANDARARREN TSARI,WANDA ZAI HASKAKA MUSU HANYA TA MUSULUNCI DA MIKAKKAR MANHAJI (YA KU MUTANE HAKIKA WATA HUJJA TA ZO MUKU DAGA UBANGIJINKU, MUN SAUKAR MUKU DA HASKE BAYYANANNE, TO AMMA WADANDA SUKA YI IMANI DA ALLAH KUMA SUKA KANKAME SHI,TO ZAI SHIGAR DA SU CIKIN WATA RAHAMA DAGA GARE SHI DA FALALA YA SHIRYAR DA SU ZUWA GARE SHI TAFARKI MIKAKKE.)
RAYUWA TA TSIYATA BAZA TA KAU BA, HAKA BA ZAA FITA DAGA WAHALHALU BA A DUNIYA DA LAHIRA  HAR SAI MUTANE SUN MIKA WUYA GA MANHAJIN LITTAFIN UBANGIJINSU,SU KUMA MIKA WUYA GA KOYARWAR ANNABINSU DA AKA TURO MUSU.
 LALLE BABBAN GINSHIKI NA GYARUWA DA RABAUTAR AL'UMAR MUSULMAI, DAIDAIKUN SU DA GABADAYANSU, SHI NE MIKA WUYA NA GABADAYA GA SHARIAR ALLAH MABUWAYI DA DAUKAKA.A KYALE DUK WANI ABU DA KAI KOMO A MIKA WUYA GA HUKUNCIN ALLAH MAI GIRMA DA DAUKAKA DA NA MANZONSA TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI.
LALLE WAJIBIN MUSULMAI SHINE GIRMAMA UMARNIN ALLAH MAI GIRMA DA DAUKAKA, DA MURAKABARSA A BOYE DA BAYYANE, CIKIN TSANANI DA SAUKI, CIKIN ABIN DA RAI KE SO DA WANDA BAI SO. CIKIN YANAYI NA CUTA DA AKASINTA, DA LOKACIN YALWA DA LOKACIN KUNCI, ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA CE, (BAI DACEWA GA MUMINI KO MUMINA IN ALLAH YA YI HUKUNCI DA MANZONSA NA WANI UMARNI DA SU KASANCE SUNA DA ZABI CIKIN UMARNINSU, DUK MAI SABA WA ALLAH DA MANZONSA TO YA BATA BATA BAYYANANNE).
WANNAN AYAR MAI GIRMA TANA KAFA MANA WATA KA'IDA NA ASALI WANDA YA WAJABA TA KASANCE TSARI NE GA RAYUWAR MUSULMAI, KUMA YA ZAUNA CIKIN ZUKATARSU, KUMA SU ZARTAR DA SHI A WAKI'INSU, LALLE SHI DIN NAN TUSHE NE MAI GIRMA WANDA KE WAJABTAWA MAI KIWO DA WANDA AKE KIWATA, GA DAIDAIKU DA KUMA AL'UMA DA SU AMSA KIRAN UMARNIN ALLAH MAI GIRMA DA DAUKAKA, DA NA MANZON ALLAH TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI, A DUKKAN YANAYI  DA SAURAN BANGARORI,DA FAGAGE NA RAYUWA DA KAI KOMO NA YAU DA KULLUM.
WANNAN AYAR TANA TABBATAR DA WATA KA'IDA MAI GIRMA, DA KE NUNA NA DAGA CIKIN ABIN DA KE HUKUNTA IMANI, DA SIFFARSA DA RUKUNANSA AKWAI GAGGAWA ZUWA GA NEMAN YARDAR ALLAH MABUWAYI DA DAUKAKA,DA NEMAN SHIRIYA DAGA KOYARWAR MANZON ALLAH TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI,DA RUSUNAWA DA SALLAMAWA DA MIKA WUYA GA HUKUNCIN ALLAH DA HUKUNCIN MANZON ALLAH TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI A DUKKAN WANI SHA'ANI NA DUNIYA DA ADDINI, HAR YA ZAMA BAWA BAI DA WANI ZABI KO GANIN DAMA WURIN ZARTAR DA UMARNIN ALLAH MAI GIRMA DA DAUKAKA DA UMARNIN MANZONSA DUK YANDA RAI DA SHA'AWE SHA'AWE SUKA KARKATA ZUWA GA WANINSA, NA DAGA CIKIN ABIN DA IMANI KE LIZIMTAWA AL'UMA MUSULMAI SU RAYU KARKASHIN INUWA NA SHARI'A MAI TSARKI, KUMA YA ZAME ABIN DA RANSA KE SO DA ABIN DA ZAI FISKANTA SHI NE BIYE WA ABIN DA YA ZO A LITTAFIN ALLAH MAI TSARKI DA SUNNAR MANZONSA  A HARKOKINSA NA YAU DA KULLUM DA DUK WANI KAI KOMO NASHI.
WANNAN SHI NE TAFARKIN MUTANEN KWARAI MASU RABAUTA, KUMA TAFARKIN MASU TAKAWA DA CIN NASARA.
IMAMU AHMAD YA RAWAITO CEWA ANNABI TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI YA NEMAWA JULAIBIB WATA MACE DAGA CIKIN ANSAR A GUN MAHAIFINTA, YA ZO A KISSAR MAHAIFIYARTA TACE; ANNABI YA RASA WANDA ZAI NEMAWA SAI JULAIBIB TO NA RANTSE DA ALLAH BA ZA MU AURA MISHI BA, SAI YARINYAR TA CE :SO KU KE KU KI BIN UMARNIN ANNABI BAYAN  SHI YA YARDA DA SHI GARE KU TO KU AURA MISHI, SAI ANNABI YA MATA ADU'A YANA CEWA :YA ALLAH KA KWARARA ALHERI GARE TA KWARARAWA, KADA KA SANYA MUSU WAHALA A RAYUWA, TO SAI TA ZAMA BA WATA MACE CIKIN ANSAR DA TA KAI TA CIYARWA.
YA KU MUSULMAI!
LALLE NA DAGA CIKIN ALAMOMI NA IMANI INGANTACCE: TSAYAWA KAN DOKOKI NA ALLAH DA LAZIMTAR BIN SUNNAR MANZON ALLAH TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI DA GIRMAMA TARIHINSA DA TAFIYA AKAN KOYARWARSA, YA ZO DAGA DA'WUS KAN CEWA YA TAMBAYI ABDULLAHI DAN ABBAS GAME DA RAKA'OI BIYU BAYAN LA'ASAR SAI YA HANE SHI, SAI IBNU ABBAS YA KARANTA WANNAN AYAR (BAI DACE BA GA MUMINI KO MUMINA BA). AN KARBO DAGA SALIM DAN ABDULLAH KAN ABDULLAHI DAN UMAR YA CE: NA JI MANZON ALLAH TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI YANA CEWA : (KAR KU HANA MATAYENKU ZUWA MASALLACI IDAN SUN NEMI IZININKU, SAI BILAL DAN ABDULLAHI YA CE ; ( WALLAHI ZA MU HANA SU. SAI ABDULLAHI YA FISKANTO YA MISHI MUMMUNAR ZAGI BAN TABA JI YA YI WA WANI IRIN SHI BA. YA CE INA BAKA LABARIN ANNABI YA CE KANA CEWA ZAMU HANA SU). MUSLIM NE YA RAWAITO.
A RAYUWAR SAHABBAI DA TABI'AI AKWAI IRIN WANNAN  DA YAWA WURIN GIRMAMA UMARNIN ALLAH DA UMARNIN MANZON ALLAH TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI DA KUMA DIMANTAR BIN UMARNINSU DA KIYAYE SABA MUSU.
YA 'YANUWA MUSULMAI!
LALLE MAGABATA NA WANNAN AL'UMA SUN FI KOWA TSANANIN TSAYUWA DON TUNKUDE DUNIYA DA KYALA KYALANTA DA RABAUTANTA DA NASARARTA, DA AMINCINTA DA ZAMAN LAFIYARTA.
AMMA LOKACIN DA SUKA TSAYA INDA ALLAH YA YI UMARNI, SUKA ZABA WA KANSU ABIN DA SHARIAR ALLAH TA ZABA MUSU SAI SUKA RABAUTA DA ALHERIN DUNIYA DA WALWALARTA DA YARDAN ALLAH A LAHIRA.
AN KARBO DAGA A'ISHA ALLAH KARA YARDA A GARE TA TA CE:( ALLAH YA JIKAN MATAYEN MUHAJIRAN FARKO YAYIN DA ALLAH YA SAUKAR DA :( KUMA SU YI LULLUBI DA MAYAFANSU AKAN ALJIHOHINSU) SAI SUKA TSAGA SAMAN MAYAFANSU SUKA YI HIJABI DA SU.) BUHARI NE YA RAWAITO SHI MUALLAKI DA ABU DAUDA DA SANADINSA INGANTACCE.  
IBNU HAJAR YACE : KWARJALLAYENSU, JAM'I NE NA KWARJALLE WATO ZANI DA SUKE DAURAWA, FADINSA : SUKA SA HIJABI WATO SUKA RUFE FISKANSU.
ABIN DA YAKE WAJIBI GA DUKKAN MUSULMI YA TSAYA GA SHARIAR ALLAH, KUMA YA HAKIMANTAR DA DOKOKIN ALLAH MADAUKAKI DA BUWAYA CIKIN ABINDA RAI KE SO KO YAKE SHA'AWA KO YAKE KWADAYINSA, IDAN RANSA YA KIRAYE SHI ZUWA GA NEMAN WANI ABU NA NEMAN DUNIYA KO WATA SHA'AWA TA JIKI TO YA YI DUBI ZUWA GA HUKUNCIN HAKAN KO YA TAFI DAIDAI DA MANHAJI NA SHARIA MAI INGANCI, KUMA YA YI GARGADI GA RANSA MAI YAWAN UMARNI DA MUMMUNA, YA NESACI RUDUWA DA WANNAN DUNIYA MAI KAREWA MAI GUSHEWA, (ABIN DA KE GUN ALLAH YA FI ALHERI KUMA YA FI WANZUWA, ASE BA ZAKU HANKALTA BA).
YAYIN DA AKA HARAMTA GIYA HARAMTAWA NA KARSHE KWATA KWATA DA FADIN SA MADAUKAKI (TO SHIN KU MASU HANUWA NE?)  A KA KARANTA WA UMAR SAI YA CE: MUN HANU MUN HANU, SAHABBAI SUKA RINKA SHEKAR DA GIYA A KWARARO SUKA FASA TUKWANENTA SUKA HANU DAGA GARE TA.
TO YA KU JAMA'AR MUSULMAI!
KU YI RIKO DA ADDININKU, KU GABATAR DA SHI AKA KO WANI ABU MAI TSADA DA KIMA SAI KU SAMU RIBA DA WALWALA KU RABAUTA (DUK WANDA KE YI WA ALLAH  DA MANZONSA BIYAYYA TO HAKIKA YA RABAUTA RABAUTA MAI GIRMA).
HUDUBA TA BIYU
YA JAMA'AR MUSULMAI!
DUK MUTUMIN DA BAI BI SHARIAR ALLAH BA KUMA YA BI SON RANSA TO HAKIKA YA ZAME DAGA HANYA YA FANDARE DAGA TAFARKIN DAIDAI MIKAKKE YA  KUMA FADA CIKIN BATA NA NESA, KUMA YA BAUDE BAUDEWA MAI ZURFI.
ALLAH MADAUKAKIN SARKI YA CE BAYAN YA AMBACI SHANIN MUMINAI  (BAI DACEWA GA MUMINI KO MUMINA IN ALLAH YA YI HUKUNCI DA MANZONSA NA WANI UMARNI DA SU KASANCE SUNA DA ZABI CIKIN UMARNINSU, DUK MAI SABA WA ALLAH DA MANZONSA TO YA BATA BATA BAYYANANNE).
GA MANZONSA TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA A GARE SHI YA NA MAGANA DA AL'UMARSA YANA KIRAN SU ZUWA GA TAFARKIN WALWALA DA JIRGIN  TSIRA, YANA MAI CEWA : (KOWANNENKU ZAI SHIGA ALJANNA SAI WANDA YA KI, SAI SUKA CE WA YE ZAI KI YA MANZON ALLAH? SAI YA CE : WANDA YA MIN BIYAYYA ZAI SHIGA ALJANNA, WANDA YA SABA MIN TO HAKIKA SHI YA KI.)
KU KIYAYE BIN SON RAI DA BIN SHAIDAN, KU NESANCI MUNANAN ABUBUWA DA DA SABON ALLAH, ZAKU SHIGA ALJANNAR MAI RAHAMA ZAKU RABAUTA DA YARDAR MAI KYAUTA.
   
  
  



الجمعة، 14 أبريل 2017

LURA DA DAUKAN IZINA

HUDUBAR JUMA'A NA  MASALLACIN ANNABI NA SHEIKH ALIYU ABDURRAHMAN ALHUZAIFI  17 RAJAB 1438 AH
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Masanin gaibi, mai juya zukata, Mai yawan gafarar zunubai, ina yabon Ubangijina da godiya a gare shi bisa ni'imominsa da ba mai iya kididdige su sai shi, Na shaida ba abin bauta wa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, mulki da kyakyawan yabo na shi ne, kuma shi ne mai iko ga dukkan komai,
Na shaida Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa ne, kuma Manzonsa ne, Mai albishir kuma Mai gargadi, ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawanka kuma Manzonka  Muhammad da iyalansa da sahabbansa  wadanda Allah ya jibince su, to madallah da majibinci kuma madalla da mai taimako,
Bayan haka ku ji tsoron Allah Mai tsarki, a sirracenku da a bayyanenku, don ya jibinci al'amuranku ya kuma gyara halayenku, domin takawa hanya ce ta mutanen kwarai da masu rabauta, rashin takawa shi ne  bayyanannen hasara, ya ku bayin Allah ku kasance daga cikin ma'abota lura da imani, ku bi tafarkin masu hankula da kyautatawa, ma'abuta lura su ne masu lafiyayyen hankali mikakke, kuma  masu lafiyayyen fidira, kuma suke amfana da wahayi,  suna fahimtar ma'anonin abin da Allah ya saukar bisa manufar Allah da Manzonsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, suna aiki da maganar Allah don  fatan ladarsa da tsoron ukubarsa, Allah Madaukakin Sarki ya ce : (kuma wadanda suka nisanci shaidanu ga bauta musu, kuma suka maida al'amari ga Allah, suna da bushara ,to, ka bayar da bushara ga bayi na . wadanda ke sauraron magana sa'annan su bi mafi kyaunta . wadancan sune Allah ya shiryar da su  , kuma wadancan su ne masu hankali)
Lura  na daga ayukan masu hankali   mai haskakawa      kuma yana daga cikin ayyukan masu basira masu gogewa  lura yana shiryarwa zuwa ga rabauta da tsira daga ayuka masu halakarwa, kuma yana datar da ma'abocin shi zuwa ga ayuka na kworai , kuma ya shiryar da shi zuwa ga hanyar mutanen kirki masu  neman  kawo gyara  kuma karshen shi yana zamewa zuwa ga alheri , wanda ya rasa lura  tunatarwa bazai mishi amfani ba  zai fada cikin halaka kuma zai bi sha'awe-sha'awen rayuka, kuma ya bi ta hanyar mabarnata sai ya zame cikin masu nadama ,  lura shi ne kaura daga wani hali da ya shude  ma'abocin ukuba da azaba  zuwa ga kyakkyawan yanayi ta hanyar nisantar sabuban ukuba da azaba  ko kuma kaura daga tarihin mutanen kworai  da abinda Allah ya karrama su da shi , zuwa da aiki da ayukan su da bin sawun su , ko kuma tunani cikin abin halittu da sanin tsirrin da suka kunsa da sifofin su da hikimar samar da su don bautawa mahaliccin su  da kebance shi da tauhidi da biyayya  albarka da daukaka ya tabbata agare shi  .
Hakika Allah mabuwayi da daukaka ya halicci halittu  kuma ya sanyawa duniya hanyoyin da suke tafiya a kai sai ya sanya da'a sababi ne na dukkan alheri a duniya  da lahira  ya sanya sabo sababi ne na dukkan sharri a duniya da lahira  shin akwai wanda ya taba zama shakiyyi sabo da biyayya ga Allah?  Ko kuma akwai wanda ya rabauta  sabo da sabawa Allah? Hakika Allah mai tsarki ya bamu kissa a littafinsa haka ma Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya bamu kissoshi  da wasu halaye  na Annabawa da Manzanni da muminai wanda a cikin shi akwai abin lura  da kuma abu na koyi ga wanda ke bayan su , da abinda akwai tsira daga ukubobi a cikin shi  da kuma rabauta da alheri  ,  da abinda akwai kyakkyawan karshe tare da shi da daga darajoji  Allah madaukakin sarki ya ce: (Lallai ne hakika abin kula ya kasance ne acikin kissoshin su  , ga masu hankali. Bai kasance kirkirarren labari ba, kuma amma shi gaskatawa ne ga abin da yake a gaba gare shi, da rarrabewar dukkan abubuwa , da shiriya da rahama ga mutane wadanda suka yi imani)  Allah madaukakin sarki ya ce  :( Sa'annan kuma muna kubutar da manzanninmu da wadanda suka yi imani  , kamar wannanne, tabbatacce ne a gare mu mu kubutar da masu imani )  Allah mai tsarki ya ce game da masu karyatawa :( Kuma suka kulla makirci, kuma muka kulla sakamakon makirci alhali su ba su sani ba . ka duba yadda akibar makircin su ta kasance  lallai mu mun darkake su da mutanen su gaba daya  . wadancan gidajen su ne wofintattu sabo da zalunci da suka yi   lallai ne a wancan akwai aya ga mutane da  suke sani).Muka  tsirar  da wadanda suka yi imani ,  kuma sun kasance suna  takawa).
Yayin da Allah ya ambaci dewa daga cikin kissoshin Annabawa tsira da amincin Allah su tabbata a gare su  a cikin suratul Shu'ara'I  ya ciken kissan  da fadin sa madaukakin sarki , bayan tsiran Manzannin sa da muminai tare da su :(  Hakika  lallai  akwai aya a cikin wancannanka, yawancin su ba su kasance muminai ba . Hakika Ubangijinka lallai shi ne mabuwayi mai jinkai )
Ibn kasir Allah ya mishi rahama ya ce: Hakika  lallai  akwai aya a cikin wancannanka.
Ai a wannan kissan da abunda ke cikinta na ban al'ajabi da taimako da karfafa ga  bayin Allah muminai akwai nuni da hujja na yanke  da hikima na kololuwa ( lallai Ubangijinka shi ne mabuwayi  )  wato wanda ya buwayi dukkan komai  kuma yayi galaba a kansa kuma ya fi karfinsa mai jinkai da halittunsa baya gaggawa ga wanda ya saba mishi sai dai ma yana sarara mishi kuma ya jinkirta mishi , sa'annan ya damke shi damka irin na mabuwayi mai iko,  Sa'id Dan Jubair  Allah ya kara mishi rahama ya ce  mai jinkai ga duk wanda ya tuba zuwa gare shi , maganan ta tike  a fadin Allah madaukakin sarki a kissan mutanen Ludu  amincin Allah ya tabbata a gare shi  lallai a cikin hakan a kwai ayoyi ga masu lura  katada yake cewa  ga masu lura Bagawi ya ambaci haka a cikin tafsirin sa mafi amfana da  abubuwan da suke faruwa na tarihi , da hikimomi na yanayi ,sai masu lura masu tunani wadanda suke koyi da  mutane na kwarai   masu neman gyara , kuma sukan bar ma'abota barna da fasadi amma shi wanda baya lura baya wa'azantuwa !  baya wa kanshi hisabi baya aiki don lahiransa addinin shi baya hanashi aikata komai , ko hankalin shi baya hana shi aikata munanan aiyuka  da laifuka wannan kamar fa dabba ne  Allah madaukakin sarki ya ce: (  ko kana zaton cewa ,  mafi yawansu suna ji , ko kuwa suna hankali ?  su ba su zama ba  face dabbobin gida  suke . A'a, su ne mafi bacewa ga hanya.)
A cikin Hadisi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gashi : (Lallai ne idan mumini yayi rashin lafiya sai cutar ta buge shi har ya mutu ,to zai zama  kaffara ne ga  zunubansa da suka shude, idan Allah ya sauwaka mishi to zai zama kankara ne ga zunubansa da suka shude, kuma wazi ne ga lokaci mai fiskantowa. Idan kuma munafuki ya yi rashin lafiya, sannan ya samu sauki to zai zama kaman rakumi ne da masu shi suka daure shi sannan suka sake shi, to bai san don me aka daure shi ba kuma don me aka sake shi ba.)  Nasa'I ne bya rawaito



 Allah bai ambaci tarihin Annabawa ba da Manzanni  da cikamakin su  Annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  face don  ayi izina da tarihin su  a yi kuma koyi da shiryarwar su da halayen su  mku bi tafarkin su  hakika Allah ya umarci Annabinsa Muhammada tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da yayi koyi da su  sai mai tsarki ya ce :(  Wadancanne Allah ya shiryar sabo da haka  ka yi koyi da shiryarwar su . )  Allah madaukakin sarki ya ce :( Sabo da haka ka yi hakuri kamar yadda masu karfin niyya daga Manzannai suka yi hakuri).
 Allah madaukakin sarki ya ce game da  muminin yasin  :( Ya mutane na ku bi Manzannin nan ,  ku bi wadanda  ba su tambayarku wata ijara  , kuma su shiryayyu ne ).  Cikamakin su Annabin mu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi wanda  Allah ya goge sauran shari'u da shi  kuma ya aiko shi da   shari'a mafi kamala   da addini , Allah ya dauki nauyi ga duk wanda ya yi riko da shi zai shiryar da shi ya bashi  kyakkyawar rayuwa  a duniya da lahira ya shigar tare da shi mafificin halitta gidan aminci  Allah madaukakin sarki ya ce : (Kuma wadannan da suka yi da'a ga Allah da Manzon sa , to wadannan suna tare da wadanda Allah ya yi ni'ima a kansu , daga Annabawa da masu yawan gaskatawa , da masu shahada da saliha  kuma wadannan nan sun kyautatu da zama abokan tafiya )  
To wani girmamawa ne ya fi wannan , to wani daukakane ya ke kusa da wannan  matsayi?, kamar yanda Allah  ya kissanta mana  kissoshin Annabawa amincin Allah ya tabbata a gare su da wadanda suka yi imani da su don muyi  koyi da su  kuma mu bi tafarkin tsira tare da su  muyi lura da tarihinsu mu kuma san halayen su  ,Allah ya kuma bamu kissan labaran masu karyata su kuma masu  musu da  gaskiya kuma masu girman kai daga binsu  wanda  suka fifita rayuwan duniya akan na lahira  masu bin sha'awe – sha'awen su da jin dadi , don fa mu yi izina da ukubar su, kuma mu wa'azantu da abinda ya faru da su  na walakacin duniya da azabar lahira kuma mu gargadu daga tsinuwan da aka tabbatar a gare su .
Allah madaukakin sarki ya ce :(Da Adawa da Samudawa ,  alhali kuwa lallai alamun azaba sun bayyana a gare su , daga gidajen su  kuma sahidan ya kawata musu ayukan su . sabo da haka ya kange su daga hanyar Allah  kuma sun kasance masu basira  .
Kuma Karuna da Fir'auna da Hamana . kuma lallai Musa ya zo musu da hujjoji, sai suka yi girman kai acikin kasa kuma ba su kasance masu tserewa ba , sabo da haka ko wannan su mun kama shi da  laifinsa: wato daga cikin su akwai wanda muka aika iskar tsakuwa a kansa ,  kuma daga cikin su akwai wanda tsawa ta kama , kuma daga cikin su akwai wanda muka birkice kasa da shi , kuma daga cikin su akwai wanda muka nutsar, ba ya yiwuwa ga Allah ya zalunce su , amma sun kasance kansu suke zalunta .
Allah madaukakin sarki ya ce :( ko wannan su ya karyata Manzanni  sai narko ya tabbata a gare su )  Allah madaukakin sarki ya ce a kissan Banu ndir :( To ku lura fa ya masu basirori,)  tarihin manzanni tsra da amincin Allah su tabbata a gare su tare da masu karyatawa na daga masu sabawa Allah da  Manzanni  mutane sun san su zamani bayan zamani , na karshe ya karba a gun na farko , wannan na daga cikin manyan hujjojin Allah akan bayinsa wurin karfafan gaskiya da sanin tauhidi  da taimakawa masu kadaita Allah  a cikin bata da shirka da gargadi daga gare  shi  amma lura da dabi'un halittu  da gano hikimanta da siffofinta  da tunani akan kirkiran da Allah ya mata da  tunani cikin  aikin  Ubangiji gayarsa da kuma fa'idansa shi ne kadaita Allah madaukakin sarki mabuwayi da daukaka da kuma bauta masa da mishi da'a , to wanda ya kebanta da halitta shi ne abin bautawa bisa cancanci . Allah madaukakin sarki ya ce : (  Kuma lallai ne da abin lura a cikin dabbobin ni'ima; muna shayar da ku daga   abinda yake a cikin cikunansu  daga tsakanin tukar tumbi da jini, nono tsantsan mai saukin hadiya ga masu sha ) Aallah madaukakin sarki ya ce :( Allah yana juyar da dare da yini , lallai ne a cikin wannan akwai abin kula da ma'abota gannai)
  "ka ce ku yi dubi me ke cikin sammai da kasa, kuma ayoyi da gargadi ba za su yi amfani ba ga mutanen da basu ba da gaskiya da Allah ba "
To shi tuntuntuni cikin halittu ibada ne ga musulmi, amma daukan izina cikin wadannan halittu yana kara wa musulmi imani, kuma yana kara mishi zurfi cikin yakini, Allah Madaukakin sarki ya ke cewa :( Lalle ne a cikin sammai da kasa akwai ayoyi ga masu imani)
Tunani da lura na tabbatar da mai shakku, yana kuma raya zukata, yana haskaka gannai, yana mikar da halaye, shi kuma kauda kai daga tunani da lura yana kekasar da zukata, yana haifar da gafala,yana ja zuwa ga nadama, yana kuma jefa mutum cikin sabo    An karbo daga Abu Huraira Allah kara yarda a gare shi ya ce : ( Lalle Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce a isra'I : yayin da na sauko zuwa sama ta duniya sai na dubi kasa ta, to sai ga wata iska da kara da hayaki, sai na ce : me ye wannan ya kai Jibrilu? Sai yace : wadannan shaidanu ne ake kona su a gaban dan Adan basu tunani ga mulkin sammai da kasa ba don haka ba da sun ga abin mamaki) Ahmad ne ya rawaito
Aallah madaukakin sarki ya ce :( Lalle ne wadanda suka yi takawa idan wani tashin hankali daga shaidan ya shafe su, sai su tuna (Allah) sai ga su sun zama masu basira. Kuma 'yan uwansu (shaidanu ) suna taimakon su a cikin bata  sa'anan kuma ba su takaitawa).
Allah sanya albarka a gare ni da gare ku cikin Alkur'ani.
 Huduba ta biyu :
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya haskaka zukatan masoyansa da Alkur'ani, ya haskaka gannansu da imani, ya kawata ayyukansu da kyautatawa,
Ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina gode mishi, bisa ga ni'imominsa da ba mai iyakance su koma bayansa,
Na shaida ba abin bauta wa da gaskiya sai Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, mulki da yabo duka na shi ne, Mai rahama mai jinkai.
Na shaida cewa Annabinmu kuma shugabanmu bawansa ne kuma manzonsa ne, wanda aka kebantar da shi da dunkulallun kalmomi masu kamalar ma'ana da cikan bayani, Ya Allah ka yi salati da aminci da albarka bisa ga bawanka kuma manzonka  Muhammad da iyalansa da sahabbansa, da wadanda suka bi su da kyautatawa
Bayan haka. Ku ji tsoron Allah Madaukaki zai gafarta muku,zai tattaro muku dukkan alheri a rayuwanku da bayan mutuwarku,
Ya ku bayin Allah ! Ku yi wa kan ku hisabi kafin a yi muku hisabi, kowannen ku ya duba game da karshen al'amari, da karewar ajali, to wanda ya yawaita lura to kurakuransa za su karanta, wanda duk ya kiyaye sabawa Allah da zunubai to zai rayu cikin aminci, kuma a datar da shi zuwa ga kyakkyawan karshe, mai samun sa'ada shi ne wanda ya waazantu da waninsa, mai hasara kuwa shi ne wanda waninsa ya waazantu da shi.
Hakika Allah ya  yi zambo ga masu bin son rai wadanda basu yi lura ba suka wa'azantu da abin da Allah ya basu na labarai, Allah Madaukakin sarki ya ce :( Kuma suka karyata kuma suka bi son zuciyarsu, alhali kuwa kowane al'amari (wanda suke son su tare daga Annabi ) an tabbatar da shi.  Kuma lalle abin da yake  akwai tsawatarwa a cikinsa na labarai ya zo musu.)
Ku saurara Allah Madaukakin sarki na da wasu hanyoyin da ya saba bada lada da alhaki akan su to duk wanda ya ci karo da sunnar Allah to za ta tambadar da shi ta tarwatsa shi ya fado ya kaskanta, Allah Madaukaki ya ce : (A kan hanyar Allah (ta gyaran jama'a) a cikin wadanda suka shude gabaninka , kuma ba za ka sami musanya wa ba ga hanyar Allah.)
Ya zo a hadisi (ku yawaita ambaton mai katse jin dadi mutuwa)

Ya ku bayin Allah : Lalle Allah da Mala'iku na salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a gare shi kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi.
  
  

 vv