الثلاثاء، 3 سبتمبر 2019

wasiyya ga dalibai


Hudubar Masallacin Annabi na sheikh Salah Dan Muhammad AlBudair.29 zulhajji 1440AH

Hudubar Farko

Ya ku musulmai
Kokari zuwa ga halaye na mutunci da kyawawan dabi'u dabi'a ce na masu juriya kuma al'ada ce na masu kokari, ilimi shi ne daukaka mai daga darajan mai nemansa kuma aga kiman ma'abocinsa a ido , duk wanda ya so ilimi to falalolin shi kuwa zai kewaye shi abubuwan adonsa su sauka a farfajiyansa. Almuzani ya ce : "na ji shafi'I Allah ya yarda da shi yana cewa duk wanda ya nemi ilimin alkura'ani to kimarsa za ta kara girma duk kuma wanda ya yi nazarin ilimin fikihu matsayinsa zai yi kyau, duk wanda ya rubuta hadisi zai zama yanada karfin hujja duk wanda ya yi nazari a ilimin lugga dabi'arsa za ta tausasa, duk wanda yayi nazari a ilimin hisabi ra'ayin shi zai yawaita duk wanda bai kare kansa ba to iliminsa ba zai mishi amfani ba" .
Al'umma na samun karfi ne ta hanyan ilimi ###  hukunci a cikin zamani ana danganta shi ne zuwa ga alkalami ###sau da yawa tokuba na zubar da jini #### alkaluma kuma na zubo da hikimomi ###da mutane za su yi a'adalci ### da falala a tsakaninsu zata kasance ne  ### ta hanyar digon tawada ba ta hanyar zubar da jini ba ### ka dukufa wurin neman ilimi #### za ka kai kololuwa a matsayi ### a falala  wanda yana kumshe da daukaka da karamci.
ilimi a lokacin fitina ya na baka kariya, a lokacinci  kadaici yana dauke ma kewa yana sanya daukaka a cikin iyalai 
ya ku musulmai:
ga sabuwar shekarar karatu ta kunno kai nan ba da jimawa ba za a bude makarantu da jami'o'i za a karbi dalibai da kauna da maraba to saboda haka ga wasu wasiyyoyi ga dalibai maza da dalibai mata game da wannan munasabar:
Ya kai dalibi to ka koma makaranta tare da kwadayin karatu da farinciki da annashuwa da himma da kokari ka cire mutuwan jiki da jin tawaya da sakaci da kasala .
samun daukaka na ga kokari ### rasawa kuma na ga kasala  ### to ka kafu za ka samu cimma burinka nan kusa  ### lallai matashi wanda ya siffantu da himma irin na mutanen farko ### kuma bai saba rage zance ko aiki ba duk wanda ya sarayarda himma to ba zai cimma bukatunsa ba ### duk wanda ya yi jifa da kifiyoyi na ji ji da kai to ba zai samu ba .
Hakika mai himma ma'aboci hankali za iya cimma gaci ta hanyar da'a ga himmarsa da kuma sabawa son rai.
ya ku dalibai : ku yi sammako ku gaggauto zuwa ga ajin karatu, na horeku da ku nesaci  jinkiri da ja da baya  domin a cikin sammako akwai albarka da samun arziki da najahi da kuma dace,  Tirmizi ya rawaito daga sakr dan gamidi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (ya Allah ka sa albarka ga alummata a cikin sammakonta , sai ya ce ya kuma kasance  idan ya tura mayaka ko kuma runduna yana turasu ne a farkon wuni sakru ya kasance mutun ne dan kasuwa ya kasance kuma idan ya tura kasuwanci yana tura su ne da jijjifi sai ya zama hanshakin mai kudi dukiyarsa ta yawaita)   
Samun albarkan rana baya tabbatuwa sai da riskan sallan asubahi domin lallai sallan asubahi tamkar wata iska ce mai kamshi da wani yanayi mai dadi ku sammaka kuma ku yi katanga da adu'oyi  na neman kariya da azkar da suka zo daga annabi wadanda suke jefa debe kewa a cikin rayi da farin ciki a cikin zuciya su kara karfi da nashadi a jiki da kariya da kiyayewa ,duk wanda ya bawa ransa rabonta na more rayuwa da mutuwan jikin da sabo da jinkiri da bacci daga barin aikin shi da makarantan shi da hissarsa na karatu to hakika zai rasa  manufarsa danashinar sa zata yi girma, duk wanda ya yawaita kwanciya to zai rasa biyan bukata wanda ya lizimci kasala to zai yi asaran fatarsa shi mutun sakali mai kasala yana rayuwa ne matsiyaci zai zama yayi nesa amma duk wanda ya yi hakuri  to zai rabauta, da hakuri ne ake bude kofofin da suke rufe kuma ayi dace.
Baccin safiya wato yin bacci baya sallar asuba ya halatta sai dai idan zai kai ga sarayar da wajibi, kuma baccin kailula wato baccin azahar mustshabbi ne saboda hadisin Anas Allah ya kara yarda  a gare shi ya ce manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce (ku yi baccin kailula saboda shaidanu basa yin baccin kailula ) abu nua'im ne ya fitar dashi 
 saboda kailula yana maida nashadi ga kwakwalwa da kuma jiki yana taimaka wa wurin bita da sauke nauyin da ya wajaba akan mutun da kuzari da kuma karfi da nashadi.
ku kiyaye kashe dare da hira domin yana haifar da wahala da kuma sa nauyin jiki kuma bala'i ne da ke bata yanayi, mutun ya kasa sakewa ya kashe mishi kuzari ya jefa mishi gajiya na zuciya da jiki kada  ka fi karfin idanunka ka hana shi barci idan barci ya zo, ka yi barci a farkon dare ka hutar da idanuwanka biyu, kada ka cutar da iyayenka,  a ko wani safiya sau da yawa mun ga wanda ya sarayar da aikin shi ko ya bar karatun shi ko kuma yayi sakaci da iyayen shi da iyalan shi sakamakon bata dare kan abin da ya ke na haram abun zargi tare da wasu abokan banza masu batarwa masu lalatarwa. ya kai dalibi ka yi kwadayin samun ladabi da tsabta da tsarkin zuciya da girmama malami da  lazimtan tsari da kiyaye abin da aka dora ma na karatu, da kiyaye wurin karatu da kuma abin da aka dora ma na karatu na makaranta, ka ji tsoron Allah domin Allah ba abin da ke boyuwa  a gare shi na zuciya ba wani kwayan zarra ko kwayan hancin dibino da zai shiga wa Allah duhu, ka sanya ilim shi ne babban tattalinka ladabi ya zama shi ne tufafinka ka kasance mafi cikan mutane ladabi, mafi tsananinsu wurin kankan da kai, kuma ka zama ka fi su tsarkaka da kuma addini ka zama ka fi su karancin shirme da kuma yawan fushi, ka abokanci mutanen kwarai ka yi nesa daga mutanen sharri, kar ka kusance su kar ka aminta da su kar ka yi cakudedeniya da su ko ka zauna da su, kada ka zauna zuwa ga mutanen banza domin halayen wawaye yana raba  mafi sharrin mutane shi ne wanda bai damu mutane su gan shi ba yana mummunan abu, duk wanda ya so yayi ababan mutunci to zai nesaci abubuwa na haramun kar ka saki ganinka kada ka kafa ganinka zuwa ga waninka domin idanuwa tarkon shaidan ne duk wanda ya saki ganin shi zai hadu da ajalin shi, na horeka kar ka kai kanka wuraren abin tuhuma da  abin da zai haifar da shakku na horeka da kar ka yi abin daza ka zo kana bada uzuri ka dauki izina daga waninka duk mutumin da luran shi ya yi yawa to kusakuren shi za su karanta, lallai rabautacce mai samun sa'ada yana da abin wa'azi ga wanin shi kuma yana mai daukan gogewa a matsayin abin da zai yi mishi hukunci  abin da zai rika lura da shi, na gargade ka da dukkan wani wasa wanda zai haifar da kiyayya ko ya zubar da kwarjini,  ba daukaka shi ne a kyakkyawan tufafi ba sai dai daukaka na nan ga ilimi ne da ladabi da addini, harshe waziri ne na mutun idan baka iya fadan magana wanda ya ke na daidai ba to ka yi shuru daga abin da yake ba daidai ba shi kanshi shi ne daidai, kada ka kasance cikin wanda ya ke aibata wa sannan ya na yawaita zagi yana yawaita suka ga abokai kada ka bankado laifukan mutane muddin sun boye sai Allah ya tona asirinka na daga laifuka, ka ambaci kyawawan abin da ka gani a cikinsu a duk lokacin da aka ambace su  kar ka aibata wani cikinsu a abin da kai ma kana da shi kar ka yi abokantaka da mai kasala, Abubakar alkawarizmi ya na cewa :" kar ka abokanci mai kasala a duk halayensa## sau da yawa mutun na kwarai kan lalace sakamakon bacin wani## raban wawa zuwa ga mai wayo abu ne da yake cikin sauri## baka ganin gaushi da ake dora shi a cikin toka shi ke nan sai gaushin ya mutu ?
A tarbiyantar da al'uma su taso kan kyawawan laduba wajibi ne da ya rataya ne a kan iyaye da majibinta al'amura,  wani daga cikin masu hikima ya ce : "ku yi gaggawa ta hanyan ladabtar da yaranku kafin shungulla su rarraba tsakaninku"
Ya ku dalibai : ku yi gaugawa zuwa ga ilimi wanda  dage mishi  ya dace agare ku, ku kiyayi hayaniya da kuma gajiya da kosawa da kasawa da yankewa .
Ka nema kada ka yi hayaniya wurin neman, laifin dalibi shi ne ya yi hayaniya ku nemi ilimi duk wanda ya nemi ilimi zai mikar da shi tun yana karami kuma zai gabatar da shi idan ya girma.
 Urwa dan zubair ya ce :" 'ya'ya na 'ya'ya na ku nemi ilimi in kun kasance kanana ba a bukatanku, to ya wuci ku zame manya  ba za a wadatu da ku ba."
ku yi kwadayi bisa makarantu domin  makarantu su ne wurin dashe, duk wanda darasi ya kwace mishi to dashe ya baci mishi, ku dimanci kallo a cikin littafi kada ku gaji daga leke leke a littafi da bincike da karatu da kuma daukan rubutu da bita da kuma mudarasa a tsakani da hadda.
Ibnul jauzi Allah ya mishi rahama ya ce : da zan ce lallai ni din nan na tsinkayi littafi littafi da ya kai mujalladi dubu ashirin kai dama sai na ce ma ya kasance ya fi haka a lokacin da na ke nema,
Ya ku dalibai  kokari kokari a tsakanin alkaluma da kuma litttatafai da tawada da abun rubutu har ku riski burinku, wasunsu suka ce na yi kura shekara arba'in ban yi kailula ba ban kwanta ba face littafi na dore akan kirji na an tambayi Imamu Ahmad bin Hanbal Allah ya mishi rahama zuwa yaushe ne mutun zai nemi ilimi sai ya ce "tare da kurtun tawada har zuwa akai shi makabarta" ya kai dalibi kasa natsuwa da bi a hankali da kaifin hankali na horeka da kar kayi gaggawa a wurin tafiya da hauka da nuna danyen kai da yaranta, wanda ke koro sharri ya jefa mutun cikin nadama hakika wanda ya bi a tsanaki zai iya riskan hajarsa wanda ya yi gaggawa kuma zai iya fadawa cikin kuskure, duk wanda ya yi amfani da wayar salula a yayin da yake tuki to hakika ya kai kansa ga hatsarin mutuwa ya kai kansa zuwa ga bakin halaka da abin da ya ke makruhi saboda waya yana dauke hankali da ji ya sa mutun ya rasa kulawa da halartowa da hankali duk mutuninda idonsa ya kafu akan waya ya saki kunnuwarsa ya sunkuyar da kansa da kafadunsa ya shagalta da tattaunawa da ture ture da yada tagrida da ababan kallo  a halin yana tafiya to hakika ya zo da wani babban laifi da wani abin da aka ki, to ka sanya tunanika ka tattaro da hankalinka zuwa ga inda ka nufa da abin da ka fiskanta da tukinka idan wani abu ya zo ma na tunani ko na sada wani zumunci ta wayarka to ka fita daga kan hanya ka tsaida abin hawanka to ka kare bukatarka da wayarka ka kame kanka daga cutar da musulmai da kuma shi kanshi sharrinka kafin wani abin ki ya faru har ya sanyaka ka yi bakinciki da nadama da hasara da kaji radadi ka ce wayane ya mantar da ni ya makantar da ni ya shagaltar da ni a wannan lokacin kuma nadama ba zata yi amfani ba bayan kafarka ta riga ta zame.
Kuyi salati da aminci bisa ga Ahmadu mai shiryarwa mai   
mai ceto ga halittu gaba daya .                       

 

Huduba ta biyu

Ya ku dalibai : girmama malami fa wajibi ne mutunta shi da kimanta shi da kankan da kai  a gare shi farilla ne na tilas, sanin falalan ilimi da gode wa mai kyau aiki ne daga cikin abubuwa na kyawawan dabi'u masu daraja dalibi na siffantuwa da ladabi a ajinsa hakama tare da abokan karatunsa domin wannan shi ne girmama ilimi da kuma ma'abotansa Umar dan kaddabi Allah ya kara  yarda agareshui ya ce : (ku nemi ilimi kuma ku ilmantar da mutane shi ku nemi ilimin mutuntawa da kuma nitsuwa ku yi tawaliu ga wanda kuka koya daga gareshi da kuma wanda kuke koyarda shi kar ku kasance masu jiji da kai na daga malammai shi malami yana cikin manyanmu ne abun girmamawa cikin manya kuma girmama manya yana cikin abnda aka samo daga hadisi)
  An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda  a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi ya ce (Duk mutuminda bai tausaya wa karaminmu ba kuma bai san kiman ko hakkin babbanmu ba to baya tare da mu)
Tashi don malami ka girmamashi ###
                                      malami ya kusa ya zama manzo .
yanzu ka san wanda yafi daukaka ###
fiye da wanda yake gina kuma ya tada rayuka da hankula ?!.
tsarki ya tabbata a gare ka mafi aherin masu ilmantarwa ### ka ilmantar da alkalami karnonin da suka shude na farko
.ka fidda wannan hankalin daga duhunsa ### ka shiryar da shi zuwa ga hanya na haske bayyananne .
katuro Annabi Musa da attaura yana mai shiryarwa ### dan batulu kuma ya ilmantar da injila .
sai ka bubbugo da mabubbuga na bayani ## sai ya shayar da hadisi kuma ya bada alkura'ani (tanzila).


الأحد، 18 أغسطس 2019

TSAYUWA A KAN TAFARKI


Hudubar Masallacin Annabi na sheikh Husain Al- Ashaikh 15-12-1440AH

Hudubar Farko
Ya ku musulmai!
Na daga cikin ni'imar Allah a gare mu da ya shiryar da mu ga wannan Addini,ya kuma sanya mu musulmai: (Ku tuna ni'imar Allah a gare ku da Alkawari mai karfi da ya yi da ku a yayin da kuka ce mun ji mun bi, ku ji tsoron Allah, lalle Allah masani ne ga abin da ke cikin zukata.)
 Ya ku wadanda Allah ya musu ni'ima da kammala hajjinsu, ya wadanda aka musu baiwan ayyukan da'a a lokutan alheri to ku gode wa Allah Mai tsarki ku tsayu a kan lazimtar addininSa. Da shari'ar sa da nisatar saba mishi  da kuma ketare iyakoki Allah madaukakin sarki ya ce ;-  ( Sai  ka daidaita  kamar yadda aka umurce ka kai da wadan da suka  tuba  tare da kai  kuma ba  masu kyatara haddi ba lallai shi mai gani ne ga abin da kuke aikatawa )
(An karbo daga Abu Sufyan Dan Abdallah As-sakafi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce ;- Na ce ya manzon Allah  ka fada mini wani fadi a musulunci wanda ba sai na tambayi wanin ka a bayan ka  ba sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce;- '' ka ce na yi imani da Allah sannan ka daidaita  ) muslim ne ya rawaito
 Lallai aikin musulmi a wannan rayuwa shi ne daidaituwa akan  kadaita Allah mai tsarki da daukaka  da dayanta bauta gaba daya a gare shi , shi kadai  adu'a ne, roko ne, fata ne , tsoro ne  da kuma kwadayi da firgici  fadi da aiki  cikin da waje  a bayyane da boye  Allah madaukakin sarki ya ce :- (ka ce lallai ne sallata  da ibada na  da rayuwata da mutuwa ta na Allah ne Ubangijin talikai babu abokin tarayya gare shi kuma da wancan aka umarce ni  kuma ni ne farkon masu sallamawa )    
Lallai ita ce daidaito wadda take sanya ka  mai tsananin kauna  ga mahaliccin ka   tsarki ya tabbata a gare shi  tare da cikan kankan da kai a gare shi wanda sha'anin sa ya buwaya  da girmamawa,  lallai girmamawa ne wanda ya kunshi kadaita Allah  wanda  yabon sa ya girmama sunayen sa sun tsarkaka  da abin da ya kebanta da shi , mai tsarki na daga  rububiyya  da uluhiyya da sunaye da siffofi  Allah madaukakin  sarki ya ce ;- (ku bi abin da aka saukar zuwa  gare ku daga Ubangijin ku , kuma kada ku rinka bin wasu majibinta baicin sa)
(Kuma (ance mini) ka tsyar da fuskarka  ga addini kana karkata zuwa ga gaskiya, kuma kada ka kasance daga masu shirka   kuma kada ka kirayi baicin Allah abinda baya anfaninka kuma baya cutarka to idan ka aikata haka saannan lalle kai a lokacin kana daga masu zalunci kuma idan Allah ya shafeka da wata cuta to ba mai yaye maka ita sai shi kuma idan yana nufinka da wani alheri to ba mai mayarda falalansa yana samun wanda yake so daga cikin bayinsa da shi kuma shi ne mai gafara  mai jin kai )
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (ka kiyaye Allah sai Allah ya kiyayeka ka kiyaye Allah za ka sameshi gaba gareka idan za ka roka ka roki Allah idan za ka nemi taimako ka nemi taimakon Allah ) tirmizine ya rawaito kuma ya ce hadisi hasan sahihi
Daidaituwa akan tafarki mai tsiratar da bayi ita ce take sanya bawa ya zama mai kushuii gaba da girman Allah  ko wace girma ke kankanta gaba da girmansa shi halitta  duk yadda ya kai ga masayi ko duk yadda ya kai ga martabansa ya daukaka to shi halattace ne kuma abin raino ne wanda ake gudanar da shi abin mallaka. Allah Madaukakin Sarki ya ce game da AnnabinSa: (Ka ce ba ni mallaka wa raina wani amfani kuma haka ban tunkude wata cuta face abin da Allah ya so, kuma da na kasance ina sanin gaibi da lalle ne da na yawaita daga alheri kuma cuta ba za ta shafe ni ba.ni ban zama ba face mai gargadi kuma mai bayar da bishara ga mutane wadanda suke yin imani).
Ya kai bawan Allah ka kwadaita daga Allah kuma ka roke shi shi kadai ba shi da abokin tarayya, ya yaye cutarka ya kawo ma amfani ya yaye ma bakin cikinka, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Idan Allah ya shafe ka da wata cuta to babu mai kuranyewa gare ta face shi, kuma idan ya shafe ka da wani alheri to shi ne akan komi mai ikon yi )  kuma Allah mabuwayi mai girma ya ce : (ko wane ne yake karba wa mai bukata  idan ya kira shi kuma ya sanya ku mamayan kasa shin akwai wani abin bautawa tare da Allah?.kadan kwarai kuke yin tuna
lalle babbar manufa na samuwarka -ya kai halitta a wannan rayuwa- shine don ka tsayu bisa tafarkin Allah mikakke akan manhaji wanda yake na rayuwarka da kuma dabi'unka da halayenka a cikin kai-komonka wahayin da aka saukar da shi yayi hukunci akanka da kuma tarihin Annabi wanda aka turo amincin Allah su tabbata agare shi, Allah madaukakin sarki ya ce: (kuma lalle wannan ne tafarkina yana madaidaici sai ku bi shi kuma kada ku bi wasu hanyoyi su rarrabu da ku daga barin hanyata wannan ne Allah yayi muku wasiyya da shi tsammaninku kuna yin takawa )
Ya bawan Allah  ka tsayu bisa ga aiki da alkura'ni mai girma da halaye kan sunnan shugaban annabawa da manzanni zahiri da badini kana mai kuduri kuma kana aiki da shi kana mai hukunci da shi kuma kana mai nema ama hukunci da shi, Allah Ubangiji tsarki da daukaka su tabbata a gare shi ya ce: (kuma ka bi abin da ake yin wahayinsa zuwa gareka kuma ka yi hakuri har Allah ya yi hukunci kuma shi ne mafi alherin masu hukunci)
 Allah Mai tsarki da daukaka ya ce :(saboda haka sai ka yi kira kuma ka daidaita kamar yadda aka umarce ka kuma kada ka bi son zuciyarsu kuma ka ce na yi imani da abin da Allah ya saukar na littafi)
Ya kai mumini ka lazimci kiyaye  dokokin Allah kuma ka tsarkake aikinka gareshi shi kadanshi ta hanyan nufatanshi da kuma nema, za ka kasance cikin walwala na har abada  da kuma aminci  cikakke da rabauta mai girma   duniya da lahira za ka zama mafi tsarkakan mutane a rayuwa  kuma za ka kasance mafi cikan ni'ima kuma za ka zama mafi jin dadin rayuwa a cikin mutane da hali mafi dadi Allah madaukakin sarki ya ce :(lalle ne wadanda suka ce Ubangijinmu Allah ne sa'an nan suka daidaitu to babu wani tsoro a kansu kuma ba za su yi bakin ciki ba)(wadannan 'yan Aljanna ne suna madawwama a cikinta a kan sakamako ga abin da suka kasance suna aikatawa )
 Ya wanda ya sarayar da lokutan alheri ya barnatawa kansa ta hanyar aikata zunubai da abubuwa masu halakarwa to ka koma zuwa ga majibincinka Allah ka saurara zuwa ga abin da zai jefa maka fatan alheri a cikin zuciyarka to ka kasa kunnuwarka tare da sauraro daga gareka wanda zai ratsa cikin zuciyarka domin shi din nan kira ne daga wurin Ubangiji wanda ke turo rahamarsa da kaunarsa ga bayinsa, lalle yekuwa ne daga gurin Ubangiji Mai tausayi ga bayinsa duk yanda zunubi ya yi girma munanan laifuka suka daukaka Allah madaukakin sarki yana cewa (ka ce (Allah ya ce) ya ku bayina wadan da suka yi barna akan rayuwarsu kada ku yanke kauna daga rahamar Allah, lalle Allah na gafarta zunubai gabadaya lalle shi, shi ne mai gafara mai jin kai )
sannan ya kwadaitar da bayinSa zuwa ga maida al'amari ga Allah da komawa gare shi kafin tserewan lokaci da sarayar da zamani domin kar a fada cikin hasara da nadama game da sakacin yin da'a ga Allah Mai rahama. Allah Madaukakin sarki yace : (kuma ku mayarda al'mari zuwa ga ubangijinku kuma ku sallama masa a gabanin azaba ta zo muku sa'nan kuwa ba za a taimake ku ba)
(kuma ku bi mafi kyaun abin da aka saukar zuwa gare ku daga ubangijinku a gabanin azaba ta zo muku bisa auke kuma ku ba ku sani ba)

Huduba ta Biyu
Ya ku bayin Allah ku tsayu kan da'a ga Allah za ku rabauta, ku lazimci koyarwar Alkur'ani da sunna zaku samu walwala, samun daukaka da shugabanci na ga lizimtar addinin Allah da bin sunnar Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma kyakkyawan karshe na ga tabbatar da tauhidi da tsoron Allah Mabuwayi abin girmamawa.   
Allah Madaukakin sarki yace : (wadanda suka yi imani kuma basu gauraya imaninsu da zalunci ba wadannan suna da aminci kuma sune shiryayyu)
Kuma kaskanci da walakanci da tabewa da hasara na cikin sabawa Allah da munanan laifuka da sabawa umarni da hani.
 Allah Madaukakin sarki yace : (kuma wanda ya sabawa Allah da ManzonSa kuma ya ketare iyakokinSa zai shigar da shi wuta yana madawwami a cikinta kuma yana da wata azaba mai walakantarwa).


   

السبت، 27 يوليو 2019

Alhurmar Aikin Haji


Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Abdullahi dan Abdurrahman Albuaijan 23/11/1440AH
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda ya tattaro zuwa gare shi wanda ya nemi mafaka, Ya tanadi Aljannar ma'awa ga wanda ya nufe shi.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, ya daidaita bisa al'arshi, kuma ya yi hukunci,lalle kowani mutum da abin da ya nufa, na shaida Annabi Muhammadu bawanSa ne kuma ManzonSa ne,bai bata ba kuma bai kauce hanya ba, kuma bai furuci bisa son rai face wahayi da ake yi masa, ya isar da sako ya bada amana ya yi wa Al'uma nasiha kuma ya yi umarni da takawa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa, da wanda ya bi su da kyautatawa ya hana rai ga soye soye rai,
 Bayan haka lalle mafi alherin zance shine maganar Allah,wanda aka saukar, kuma maga mafi gaskiya ita ce :
Ku saurara dukkan kome abin da ya ke ba Allah ba bata ne, kuma mafi alherin shiriya shi ne shiryarwar Annabi Muhammad dan Abdullah abin fifitawa, kuma mafi sharrin zance shi ne fararrun  mai kirkirare da ya zama bidiah, ko jahili mai wauta mai batarwa,ya ku bayin Allah, ina muku wasiyya da ni kai na da ku ji tsoron Allah don ita ce wasiyar Allah ga mutanen farko da na karshe, ( Hakika mun yi wasiya ga wadanda aka bawa littafi gabanninku da ku kan ku da ku ji tsoron Allah)
 Ya ku musulmai! Lalle Allah na halittan abin da ya so ya kuma yi zabi, hakika ya zaba cikin mala'iku manzanni da kuma cikin mutane.
Ya fifita ramadan bisa sauran watanni na lokaci, ya zabi Daki mai alfarma ya sanya shi dakin farko da aka sanya wa mutane,ya fifita shi ya sanya shi mazauni ya sanya shi gun samun lada da aminci ga mutane,da aminci ya albarkace shi ya sanya shi Alkibla,ya tattale shi ya ba shi alhurma,ya girmama shi ya sanya shi wurin ibada na tushe, (Allah ya sanya kaba daki tsararre ma'aunin Addini ga mutane)
Ya sanya Alhurma ga shingensa, ya sanya shi daki dadadde ya kira zuwa ga a nufe shi,Ibrahim ya ce : (ka  shelanta ga mutane a hajji za su zo ma a tafe da akan abin hawa zasu zo daga kowane sako)
             Ya ku musulmai! Ku amsa kiran Allah " mun amsa kiranka ya Allah kuma mun amsa kiranka ya Allah! Mun amsa kiranka ba ka da abokin tarayya ya Allah mun amsa kiranka! Lalle dukkan godiya da ni'ima naka ne kuma mulki ma naka ne baka da abokin tarayya.
Ya ku bayin Allah! Lalle musulunci Akida ne da Ibadoji da dabiu da halayya an gina shi akan abubuwa guda biyar, ; rukunnai wadanda sune tushe :Ta An karbo daga Ibnu Umar Allah ya kara yarda a gare shi da mahaifinsa ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : "An gina musulunci a kan abubuwa guda biyar; Akan su kadaita Allah da tsaida sallah da bada zakka da Azumin watan ramadan da hajji"Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
  
 Ya ku mutane!Lalle Allah ya wajabta hajji  a gare ku, to ku yi hajji,  Allah Madaukakin sarki yace (kuma akwai hajjin Dakin domin Allah, akan mutane ga wanda ya samu ikon zuwa gare shi)
Hajji ibada ce ta rayuwa, kuma karshen al'amari da cikan rukunan musulunci, a ciki ne Allah Mabuwayi da daukaka ya saukar da
(A yau na kammala muku Addininku,kuma na cika ni'ima ta a gare ku, kuma na yard da musulunci ya zama addini a gare ku)
An karbo daga Abu Said Alkudri cewa Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :; Allah Madaukakin sarki ya ce;Lalle bawa na na bashi lafiyan jikin shi, kuma na yalwata mishi a rayuwa, shekaru biyar bai zo gare ni to lalle hasrarre ne) Ibnu Hibban ne ya fitar da shi a sahihinsa.
   Ku sauke farillun Allah, ku nufi dakin Allah (kuma ku cika hajji da umara domin Allah!)
Ya ku bayin Allah!
Hajji rukuni ne na wajibi kuma farilla ne na dole Alkur'ani mai girma ya yi nuni ga hakan da muhimmin labari mai girma, Hajji na cikin ibadoji mafi daraja, da ayyuka mafi girma  na neman kusancin Allah, da masa biyayya, yana daga darajoji yana goge kusakurai yana kankare munanan laifuka har da manyan su.An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : na ji Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa: Duk wanda ya yi hajji don Allah bai yi jima'i ba kuma bai yi fasikanci ba zai koma kamar ranar da mahaifiyarsa ta haife shi) Bukhari ne ya rawaito.
 Kuma Tirmizi ya rawaito a littafinsa Assunan ya ku inganta shi daga Abdullahi dan Mas'ud Allah ya kara yarda a gare shi ya ce ;Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ku biyar da hajji da umara domin suna gusar da talauci da zunubai kamar yadda zuga zugi ke tafiyar da dottin karfe da zinari da azurfa.Hajji mabrur bai da sakayya sai Aljanna)
Ya zo cikin sahihu Muslim daga Abu Huraira an tambayi Manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ko wani aiki ne ya fi falala? Sai ya ce :Imani da Allah:aka ce sa'anan sai me? Sai yace : jahadi a tafarkin Allah sai aka ce sai me? Sai ya ce : Hajji Mabruri)

Ya ku jama'ar musulmai!
Lalle Allah mai tsarki ne bai karba sai mai tsarki, to duk wanda ya nufi aikin hajji to ya kame daga Haram, to ya zabo daga dukiyarsa halal, An karbo daga Abu Huraira yace Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :( Lalle Allah Mai tsarki ne bai karba sai mai tsarki, lalle Allah ya umarci muminai da abin da ya umarci Manzannai sai ya ce (ya ku Manzannai ku ci daga tsarki kuma ku yi aiki na kwarai lalle ni masani ne ga abin da ku ke aikatawa) kuma ya ce: ( ya ku wadanda suka yi imani ku ci daga mai tsarkin abin da muka azurta ku) . sai ya ambaci wani mutum yana tsawaita tafiya mai gashi a tsatsaye da kura yana daga hannayen shi sama yna cewa : Ya Ubangiji na ya Ubangiji na a halin abincinsa na haramun ne, abin shansa na haramun ne, kuma tufafinsa na haramun ne kuma an ciyar da shi abin kalace na haramun.
Allah ya sanya ni da ku cikin wadanda suke jin magana su bi mafi kyansa, wadannan su  Allah ya shiryar wadannan su ne ma'abota hankula.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah da ya bada kuma ya ni'imta, ya kuma shiryar zuwa ga shiriya kuma ya yi ilhama, ya bayyana daidai ya kuma fahimtar,ya sanya hajji mafi darajan aiki kuma mafi girma,
 Ya ku musulmai!
Lalle kuna wata mai alfarma da Allah ya shar'anta alfarmanta ya girmama shaninta ya yi gargadi game da zalunci a cikinta sai ya ce:( Lalle kidayan watanni a gurin Allah guda shabiyu ne a littafin Allah a ranar da ya halicci sammai da kasa, daga cikinsu akrajab da muwai guda hudu nasu alfarma) uku daga cikin su a jere suke Zulka'ada da zulhajji da Muharram da rajab,na mudar. Sannan ya ce wannan wani wata muke ciki sai muka ce Allah da ManzonSa ne suka fi sani sai ya yi
Shuru har sai da muka tsammaci zai ambace shi da wani sunan ne, sai yace ase ba zulhajji ba ne sai mka ce : E sai yace wani gari ne wannan sai muka ce Allah da ManzonSa ne suka fi sani sai ya yi shuru har muka zaci zai ambace shi da wani suna da ba shi ba sai yace Ase ba wannan bane gari mai alhurma? Sai suka ce e shine.sai yace to a wace rana muke?sai suka ce Allah da Manzonsa ne suka fi sani. sai ya yi
Shuru har sai da muka tsammaci zai ambace shi da wani sunan ne, sai yace ase ba a ranar suka muke ba? Sai suka ce: E   haka ne sai ya ce : To lallai jininku da dukiyanku da mutunci a gare ku haramun ne, kamar alhurma wannan ranar taku a wannan gari naku a wannan wata taku., za ku hadu da Ubangijinku zai tambaye ku game da Ayyukanku, ku saurara : kada ku koma a baya na kafurai sashinku na dukan wuyan sashi, to ku saurara wanda ya ke nan ya sanar da wanda bai nan, don ta iya yiwuwa wanda za a isar zuwa gare shi ya kiyaye fiye da wanda ya jiyo.ku saurara! Shin ko na isar da sako, shin ko na isar da sako) Bukhari da muslim ne suka rawaito.
Lalle watan zulkida shine watan farko cikin watanni masu alfarma da suke hade, a cikinsa ne Annabi ya kasance ya yayin da mushrikai suka hana shi shiga,da umaran da ya yi a shekaran da ta kewayo a zulkida ne ya yi ta a lokacin da ya yi sulhu da su, azulkada a yayin da ya yi sulhu da su, da umarar ji'irrana wanda ya raba ganimar hunain,da umara da ya yi da hajjinsa.  Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Ya ku bayin Allah !
lokaci na hajji lokaci ne na biyayya da da'a da kyauta, kuma karama ce  samun kyautar,
ya kasance a jahiliyya abin alfahari ne shayarwa ga Alhazai da suturce kaba da bata kulawa.suna munafasa a cikinta, da musulunci ya zo sai ya tabbatar da haka, Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shiya yiwa Abbas izini da ya kwana a makka a dararrakin kwanan mina don shi,ya zo gurin da ake shayarwa  da ya nemi da a shayar da shi kuma ya sha ya tafi ta gun masu zamzam a halin suna shayarwa suna aiki sai yace (ku yi aiki lallai kuna kan aiki na kwarai,)  yace (Ba don kar a yi galaba a kanku ba da na sauka har na sa igiya a nan fa ya yi nuni ga kafadansa) Bukhari ne ya rawaito.
Allah ya yi gyadan dogo ga kasar Saudiya cikin hidima da ta ke yi na wurare masu tsarki, da amintar da shi ga masu dawafi da masu itikafi da masu rukui da sujada, ya mata baiwa na hidima da karbar bakuncin Alhazai da 'yan umara da masu ziyara ko shige da fice, tare da tausaya musu da gabatar da hidima da ta dace a gare su, da agaza musu wurin sake nauyin ibadojinsu,da shinfida musu dukan wata hanya ta aminci da zaman lafiya gare su, to Allah ya saka wa jagororinmu da shugabanninmu da sakayya mafi  alheri da cika da kamala da kyau da tsarki, bisa abin da suke tashi da shi na hidima ga masallatayya biyu masu alfarma da daukaka da masu tahowa gare su.
Ya ku bayin Allah! Ku kuna guri ne da ya fi soyuwa a gurin Allah, to ku bada hadin kai wurin ganin ku taimakawa ma'aikata masu tsare tsare da hidima, Allah ya karba mana ni da ku, ya mana gamon katar.
Alhazai ga daki mai alfarma,…
Hakika kun yi kokari kun yi dace na amsa kiran Allah na haji wajibi, to ku dage wurin yinta da cikata bisa yadda zaa karbe ta, ku nemi sanin hukunce – hukuncenta, na gargade ku da ku nesaci jima'I da fasikanci da jayayya (Haji watanni ne sanannu to duk wanda ya shiga aikin haji cikinsu babu batsa ko fasikanci ba musu a hajji)
   Ku sa nitsuwa da tsanaki, ku yi aikin jinkai idan an samu cunkoso, ku yi nesa da turereniya, ku tausayawa masu rauninku,domin a dalilinsu ne ake azurta ku a baku nasara.
 An karbo daga jabir yace Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya goyi Usama abayansa ya taso daga Arfa yana matse linzami dabbarsa Alkaswa kanta na taba tankin dabbar ya na nuni da hanunsa na dama da (ya ku mutane Natsuwa natsuwa) a duk lokacin da ya zo wani dutse daga cikin duwatsu sai ya dan saki linzami gareta har ta haura har ya iso muzdalifa) .Muslim ne ya rawaito


الأحد، 30 يونيو 2019

kuma abin da ya ke a gare ku na ni'ima to daga Allah ne


Hudubar Masllacin Annabi na shaikh Abdulbari Bin Awad Assubaiti 25/10/1440Ah 28/6/2019Ac
Ni'imomin Allah ga bayinSa suna da yawa ba za'a iya iyakance su ba,mai dunbin yawa ne da ba za a iya kwalkwale su ba, suna bibiyan juna basu karewa :Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Allah ne wanda ya halicci sammai da kasa, kuma ya saukar da ruwa daga sama sa'anan ya fitar game da shi daga 'ya'yan itace, arziki  domin ku, kuma ya hore jirgin ruwa yayi gudu a cikin teku da umarninSa, kuma ya hore muku koguna.kuma ya hore muku rana da wata suna madawwama biyu, kuma ya hore muku dare da wuni. Kuma ya baku dukkan abin da ku ka roke shi, kuma idan kun kidaya ni'imar Allah ba za ku lissafe ta ba, lalle ne mutum hakika mai yawan zalunci ne mai yawan kafurci ).
Samuwan abubuwa masu amfani da tunkude  cutarwa da ma dukkan alheri da bawa yake samu ni'ima ce daga Allah zuwa gare shi ; na ilimi da imani da aiki da zuriya da masauki da abin hawa da walwala da nasara Allah Madaukakin sarki ya ce (kuma abin da ya ke a gare ku na ni'ima to daga Allah ne) kuma lura da abin da ya ke kewaye da mu yana kaimu ga jin niimar Allah , Allah madaukakin sarki ya ce (To mutum ya duba zuwa ga abincinsa) kuma ya ce (To mutum ya duba daga me aka halicce shi).
Muminai na dubi ga ni'imar Allah na ciki da na waje: hakan sai ya kara musu imani ya kusanto da su ga Ubangijinsu suna masu ikirari da baiwarsa da alherinSa da falalarSa a gare su, Allah madukakin sarki ya ce : (suna yin gori gare ka don sun musulunta, kace kada ku yi gorin kun musulunta a kai na, Aa Allah ne ke yi muku gori domin ya shiryar da ku ga imani, idan kun kasance masu gaskiya.)
Mumini da kaifin hankalinsa da nunan tunaninsa; na dubi ga ni'imomin Allah da ke kewaye da shi, Allah madaukakin sarki ya ce yana mai sifanta halin muminin da zai karbi aikinsa : (Har a lokacin da ya kai ga mafi karfinsa,kuma ya kai shekara arba'in yace ya Ubangiji na! ka kange ni, domin in godewa ni'imarka, wadda ka ni'imta a kaina, da kuma a kan mahaifa na biyu, kuma domin in aikata aikin kwarai, wanda ka ke yarda da shi)
 Idan zuciyar bawa ta cika da imani; ni'ima ta godiya ga ni'imar sai ta tabbatu a gare shi, sai kai komonsa  su gyaru halayensa su tsarkaka,sai ya yi dace, Allah madaukakin sarki ya ce yana mai gori ga bayinSa: (kuma Allah ya soyar da imani a gare ku, kuma ya kawata shi a cikin zukatanku, kuma ya kyamatar da kafirci da fasikanci da sabo zuwa gare ku, wadannan sune shiryayyu. Bisa ga Falala daga Allah da ni'ima, kuma Allah Masani ne Mai hikima).

Ikirari da ni'imar Allah na daga cikin abin da ke hukunta tuna ni'imomin Allah, da kuma jingina su ga wanda ya bada su - daukaka ya tabbata a gare shi,- wanda ke dakon ni'imomi to ba zai gushe ba yana tuna mai bada su, wanda shi ne Allah Madaukaki  Mai ni'imtarwa da dukkan ni'imomi wadanda muke jujjuyawa a cikinta,
Yin ikirari da ni'imar Allah shine mabudin dukkan Alheri, zai sanya harshen mumini yana furta (Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai. Mai mulki ranar sakayya)  a tsawon wuninsa da darensa.
Idan musulmi ya tabbatar da ni'imar Allah a kan sa, ya yi ikirari da falolin UbangijinSa da ke kewaye da shi,; to lalle zai yi amfani da wadannan ni'imomin wurin neman yardar Allah Madaukaki, ga Annabi Sulaiman Amincin Allah ya tabbata a gare shi yana rokon UbangijinSa; (ya Ubangiji ka cusa mini in gode wa ni'imarka, wadda ka ni'imta ta a gare ni, da kuma ga mahaifana biyu, kuma in aikata aiki na kwarai, wanda kake yarda da shi, kuma ka shigar da ni sabo da rahamarka a cikin bayinka salihai,)
Ga Annabi musa abokin maganar Allah yana kulla alkawari ga Ubangijinsa     ; ( Yace Ya Ubangiji! Domin abin da ka ni'imta shi a kai na saboda haka ba zan kasance mai taimako ga masu laifi ba)
Idan musulmi ya tabbatar da ni'imar Allah a kan sa, to zai bayyana wadannan ni'imomin ne halin yana mai godiya da yabo, ba yana mai alfahari da girman kai ba, Allah madukakin sarki ya ce:    (kuma amma ni'imar Ubangijinka sai ka fada (domin godiya). Wato ka labarta wa mutane abin da Allah ya ma na ni'ima kana mai girmama wa ga Mai ni'imtarwan.
Ya zo a hadisi ( Idan Allah ya yi ni'ima ga bawa to yana so ya ga gurbin ni'iman a gare shi).Baihaki ya rawaito da isnadi hasan.
An karbo daga Abul Ahwas Aufu dan malik dan Nadlah daga Babansa yace :( Na zo ga Manzon Allah a halin ina wani yanayi na tufafi mara fasali, sai ya ce : kana da dukiya? Sai na ce :E, sai yace daga wani irin dukiya? Sai na ce : daga dukkan nau'i Allah ya bani; na daga rakuma da bayi da dabbobi, sai yace : To idan Allah ya baka dukiya ta aga hakan tare da kai).Ibnu Hibban ya rawaito a sahihinsa
  Idan ni'imomi sun tattaru ga rayuwar bawa ;to fa wani albishir ne na alheri ga ma'abocinsu muddin ya fahimci hakkinsu da ke kan shi kuma ya sauke wajibi, kuma ya sarrafa su ta hanyar da ke nuna godiya da bauta ga Allah.Amma wanda ya rudu da kansa ya yi jiji da kai da abin da Allah ya bashi na ni'ima har ma ya jinginta ta ga kansa kamar yadda Allah ya ambata a kur'ani bisa harshen Fir'auna yayin da ya ke cewa : (kuma Fir'auna ya yi kira a cikin mutanensa, yace : ya mutane na! ashe mulkin masar ba a gare ni yake ba? Kuma wadannan koguna suna gudana daga karkashi na? ashe ba ku gani ba)
 Haka ma Karuna yace( An bani shi akan wani ilimi wanda yake gare ni kawai)
To irin wannan ni'imar ce take juyawa azaba alherinta ya zama sharri samunta ya zama bala'i.
Mafi girman godiya ita ce gaggauta wa zuwa ga ibada Allah yace (A'a Allah kadai zaka bauta wa kuma kasance cikin masu godiya).
To kuma idan bawa ya yi kokari wurin bautawa Ubangijinsa yana mai godiya a gare shi bisa ni'imominsa, to lallai sakayyarsa a gurin Allah na daga cikin irin aikin da ya yi. Allah Madaukakin sarki ya ce : (Lalle wannan ya kasance sakayya a gare ku, lalle aikin ku ya kasance abin godewa).
Bawa ba zai iya sauke nauyin godiyan ni'immomi ba duk yadda ya yi kokari , ya isan mishi ya yi kokari ya samu yardan Allah Madaukaki! Ya samu ya yi godiya na gabadaya da godiya na musamman, a duk lokacin da ni'ima ta sake samuwa sai ya sake mata sabuwar godiya. Ya zo a hadisi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce (wanda ya ce idan ya wayi gari; Ya Allah abin da ya wayi gari da ni na ni'ima ko wani daga cikin halittunka to daga gareka ne yake kai kadanka baka da abokin tarayya kuma dukkan yabo da godiya naka ne to hakika ya sauke nauyin godiya na wannan rana, wanda ya ce idan ya yi yammaci Ya Allah duk abin da ya yi yammaci da ni na ni'ima ko daya daga cikin halittunka to daga gareka yake kai kadanka baka da abokin tarayya, to yabo da godiya ya tabbata agreka to hakika ya sauke nauyin godiya na wannan dare).
kuma  (An karbo daga Rifaa dan Rafi' Azzuraki ya ce mun kasance wata rana muna salla a bayan Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yin da ya daga kansa daga ruku'u kuma ya ce :Allah ya amsa ga wadanda suka gode mishi sai wani mutum a bayan shi ya ce:Ubangijinmu godiya ta tabbata gareka ,godiya mai yawa tsarkakakkiya mai albarka a cikinta yayinda Manzon Allah ya idar da sallah sai ya ce: wanene yayi magana dazu? sai wanan mutumi ya ce nine ya manzon Allah! sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce hakika naga mala'iku talatin da dori suna rige rige waye zai fara rubuta ta )Hakim ne ya rawaito da ibnu hibba da isnadi ingantacce
 Musulmi zai yi gaggawa zuwa kofan adu'a yana rokon Ubangijinsa da ya mishi ilhama na godiya, domin ya kankare tawaya da nakasa, ababin niimomi (kuma ka samu masu godiya bisa niimarka masu kuma kyawtata yabo da ita agare ka to ka karbe ta ka cikata agare mu )Ibnu Hibban ne ya rawaito.
Amma wanda idonsa ya makance daga ganin ni'imomin Allah to hakika wannan ya fada  rabon shaidan da waswasinsa da makircinsa, kura'ani ya hakaito hakan daga gare shi (saannan zan zo musu daga gaba garesu kuma daga baya garesu kuma daga damansu da kuma hagunsu ba za ka samu mafiya yawansu ba suna masu godiya)
Musulmi na gafala daga riskan ni'imomin Allah a gare shi yana mai   rainata ma a lokacin da ya ga abin da ke hanun wasu na ni'imomi. A cikin sahihu muslim daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(ku yi dubi zuwa ga na kasa da ku kar kuyi dubi zuwa ga wanda ya ke sama da ku domin haka ya fi dacewa don kar ku rena niimar Allah a gare ku.
Na daga cikin munanta ladabi ga  Allah dulmuya cikin ni'imomi da manta Mai yin ni'imar da kuma zurfafa wa cikin farin ciki da manta Mai yaye bakin ciki  da bacin rai, Allah Madaukakin sarki ya ce (kamar wancan ne Allah ya ke cika niimarsa a kanku tsammaninku kuna mika wuya )
(To idan sun juya to abin da ya wajaba a kanka shi ne isarwa bayyananniya) (suna sanin niimar Allah sa'annan kuma suna musantawa kuma mafi yawansu kafirai ne )kuma ya ce: (kuma wanda ya musanya niimar Allah bayan ta zo mishi to lalle ne Allah mai tsananin ukuba ne).
                 
                           Huduba ta biyu
 Mai hankali ya na kiyaye amfani da  ni'imomin Allah ba tare da ya yi sakaci da hakkin Allah a ciki ba  da bauta da godiya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Idan ka ga Allah yana baiwa bawa abin da ya ke so alhali shi kuma bawan yana saba mishi to lalle hakan a gareshi daurin talala ne sannan sai aka yayeta da wannan ayan(saannan kuma A lokacin da suka manta abin da aka tunatar da su da shi sai muka bude a kansu kofofin dukkan kome har a lokacin da suka yi farinciki da abin da aka basu, muka kama su kwasam, sai gasu sun yi tsuru- tsuru, sai aka katse karshen mutanen,wadan da suka yi zalunci, kuma godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai ) Ahmad da Baihaki ne suka rawaito Albani ya inganta shi.

Kuma musulmi na sanya bautarsa a hade da abin da ya ke riska na ni'ima, idan an bashi ni'ima sai ya yarda in an dauke sai ya yi fushi, to wannan sifa ce abin zargi,
 Allah Madaukakin sarki ya ce (kuma cikin mutane akwai mai bauta wa Allah bisa gefe, sa'annan idan wani alheri ya same shi sai ya natsu da shi, kuma idan wata fitina ta same shi sai ya juya baya akan fuskarsa ya yi hasarar duniya da lahira.
An karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah kara yarda a gare su, yace: (kuma cikin mutane akwai mai bauta wa Allah bisa gefe,) Mutum ne zai zo Madina idan matarsa ta haifi da dokin sa ya haihu sai ya ce : wannan Addini ne mai kyau, idan matarsa bata haihu ba dokin sa bai haihu ba sai ya ce : wannan mummunan addini ne).

الجمعة، 21 يونيو 2019

kofofin tuba


Hudubar Masllacin Annabi na 11-10 -1440AH/14-6-2019 AD na Sheikh Abdullah bin Abdurrahman Albu'aijan.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode masa muna neman taimakonsa muna neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi duk wanda ya batar da shi ba zaka sama mishi majibinci mai shiryarwa ba.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, ya halitta kuma ya daidaita abin halitta ya kaddara (abin da ya so) ya shiryar, na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma manzon sa ne, wanda ya turo shi da gaskiya da shiriya, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da duk wanda ya bi sawun shi,ya bi tafarkinsa da kyautatawa har zuwa ranar sakayya,
Bayan haka: Lallai mafi alherin zance shi ne littafin Allah, kuma mafi alherin shiryarwa shine shiryarwa Muhammad dan Abdullah, Mafi sharrin al'amura sune fararrunta, dukkan fararrun abubuwa bidiah ne, dukkan bidiah bata ne dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah … ku ji tsoron Allah cikin abin da ya umarta, ku hanu daga abin da ya hana ya tsawatar, ku sani dukkan karami da babba ana rubuta shi, (ya ku wadanda suka yi mani ku bi Allah da takawa, kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma ku bi Allah da takawa lalle Allah mai kididdigewa ne ga abin da ku ke aikatawa,)
Ya ku bayin bayin Allah!
Lokaci na albarka da falala da alheri da da'a ranakunsa ya kare an nade ayyukansa, lalle wata ne mai girman falala, tasirin sa a cikin Al'uma na da ban mamaki, masu nasara cikin shi sun ribata,masu kokari cikinsa sun samu ganima,ina ma da mun san wanda aka karbi ayyukansa mu mishi barka! Wane ne baa karba mishi ba mu jajanta mishi,
Madalla da farincikin wanda suka rabauta, Allah ya musu ilhamar tuba, ya datar da su ga biyayya, muna roka musu Allah da ya karba musu ya dora su kan daidai.
Ya  kaiton hasarar wadanda suka rasa wannan alheri aka katange  su daga Ubangijin su, damammaki a rayuwa suka kwace musu.ga lokutan alheri basu ribaci komai ba sai hasara da nadama,
Sai dai ya jama'ar musulmi ! kofofin tuba basu gushe ba suna bude ba a rufe su ba bayan watan ramadan,Ubangijinmu mabuwayi da daukaka yana karbar tuba daga bayin sa a kowane zamani da guri  (Shi ne yake karbar tuba daga bayin sa kuma yana yafe munana, kuma ya san abin da kuke aikatawa).
     Ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :Lalle Allah ya fi farinciki   da tuban bawansa mumini  akan mutumin da  yake cikin kasa ta sahara wacce  ke da ababan halakarwa   yana tare da dabbarsa  abin cin shi da abin shan sa na kanta   sai ya yi bacci , da ya farka sai ya ga ta tafi  ya yi ta nemanta  har sai da  kishi ya cimmasa  sai ya ce bari na koma wurina da na kasance a cikin shi  sai na je na yi bacci har ma na mutu  sai ya dora kanshi  a bisa damtsen shi don ya mutu yana halin haka  sai ga dabbarsa a kan sa  tare da ita ga guzurin shi da abin cin shi  da abin shan sa  sai  ya rike linzamin ta yayi kuskure don tsananin farin ciki yana mai cewa ya Allah kai ne bawana ni ne Ubangijin ka  .
An karbo daga Abu Huraira  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:(Idan wani yanki na dare ya shude ko kuma wani sulusin  shi , Ubangijin mu mai tsarki da daukaka zai sauko  zuwa ga  sama na  duniya  sai ya ce:-
Ko shin akwai mai tambaya na ba shi , ko shin akwai mai roko na amsa mishi , shin akwai mai neman gafara a gafarta masa har gari ya waye  . Muslim ne ya rawaito)
Zuwa ga wanda daman ramadan ya kwace mishi  to ka yi gaggawa zuwa ga tuba  kafin lokaci ya tsere   da kuma shammatan ajali kada ka yanke tsammani don duk dan adam mai kuskure ne  abin zargi  na ga wanda ya doge  kuma alhali yana da Ubangiji mai gafarta zunubai kuma bai nemi gafarar sa ba , ba don kun kasance kuna kusakurai ba kuma kuna neman gafara da  Allah ya tafiyar da ku ya kawo wasu mutane wadan da suna kuskure kuma suna neman gafara sai Allah ya gafarta musu .
YA KU BAYIN ALLAH:
Ku ji tsoron Allah kuma ku nemi gafarar sa  kuma ku koma zuwa gare shi ku mar da'a  kada ku jinkirta tuba domin  mutuwa na zuwa bagtatan  .
Allah madaukakin sarki ya ce :-(Ku tuba suwa ga Allah gaba dayanku ya ku muminai  ko za ku  rabauta)
Kuma ya ce :-( Ka ce  ya ku bayi na wadanda suka   barnatawa kawunan su  kada ku yanke tsammani daga rahamar Allah lallai Allah yana gafarta zunubai baki daya  lallai shi mai gafara ne kuma mai jin kai .  Ku koma zuwa  ga Ubangijinku  ku mika wuya gare shi  kafin azaba ya zo muku  sa'annan ba za a taimaka muku ba , ku bi mafi kyaun  abin da aka saukar gare ku daga Ubangijin ku  tun kafin azaba ya zo muku  bagtatan a halin kuna baku sani ba  kada rayi ta ce  ya hasara ta  bisa  abin da na yi sakaci a janibin Allah  , ko da na kasance cikin  wadan da suke masu isgili  ko kuma ta ce ina ma da Allah ya shirye ni  da na  kasance cikin masu takawa  , ko kuma ta ce ya yin da ta ga azaba  ina ma da ina da kome da na kasance cikin masu kyautatawa 

YA KU MUSULMAI:
Lallai ibada na da tasiri  cikin halayen ma'abocinta Allah madaukakin sarkiya ce :-(Lallai sallah na hani ga alfasha  da munkari)
Na daga cikin alamomin karban ayyuka  akwai canzawan halayen zuwa mafi kyan hali  a daya bangaren kuma  yana daga cikin alamomi na  rasa alheri da rashin karban aiki  akwai komawa baya  daga da'a  bayan shudewan ramadana  yanayin halaye ya canza zuwa mafi muni  domin sabo sashi na janyo sashi , madalla da kakkyawa bayan mummuna  sai ta goge ta  mafi kyaunta kuma shi ne kyakkyawa bayan kyakkyawa  tana mai binta , ku roki Allah tabbatuwa akan da'a har zuwa mutuwa  kuma ku nemi tsarin Allah  daga juyawar zukata  haka nan kuma daga warwarewa bayan daurewa .

 Abin mamaki da munin  kaskanci  na sabo  bayan izza ta da'a  tir da  talauci na  kwadayi bayan wadatuwa da wadatan zuci  ku roki Allah tabbatuwa , ya tabbata daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Lallai dayanku  zai yi aiki irin na 'yan aljanna  har sai ya kasance tsakanin shi da ita  face zira'I  sai littafin sa ya rigaya  , sai ya yi aiki irin na 'yan wuta sai ya shige ta ,  kuma lallai dayan ku zai yi aiki irin na 'yan wuta   har sai ya kasance tsakanin shi da ita face zira'I sai littafin shi ya rigaya sai ya shigeta  Buhari ne ya rawaito)
Ina fadin abin da kuke ji ……….

HADUBA TA BIYU

Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga Allah wanda  yake karban tuba daga bayin sa  kuma yake yafe kusakurai kuma ya san abin da kuke aikatawa ,  kuma yana amsa kiran wadan da suka yi imani kuma  suka yi aiki na kwarai   kuma yana kara musu daga falalar sa .
 YA KU MUSULMAI :
Watanni dukan su lokuta ne na ibada  ko da sun sha banban  sun saba a wurin fifiko  da ayyuka  rayuwa dukkanta   dama ce ta aiki  da biyayya   ko wanne yana wayan gari yana mai saida kan sa akwai mai 'yantata akwai kuma mai halakata ,  kuma kowa ana yassare mi shi abin da aka halicce shi  akanta   , .
To ku sabarwa kawunan da da'a ku nemi taimako game da ita da tuba  da neman gafara  da komawa zuwa gare shi da marairaicewa  da kuma murakaban Allah  guda mai rinjayi  a sirri kuma da bayyane a dare da wuni .
 (Ku bar  sabo na zahiri da na badinin  sa  lallai wadanda suke aikata laifi za a sakanya musu da abinda suka kasance suna aikatawa)
YA KU BAYIN ALLAH:
Ku rantawa Allah rance kyakkyawa , ku kaddamarwa kawunan ku abu mai amfani , (Duk wani abu da za ku kaddamar wa kawunan ku na alheri za ku same shi a wurin Allah).
(Wane ne zai rantawa Allah rance mai kyau sai ya ribanya mishi ribanyawa mai yawa).
Sannan ku sani cewa azumi garkuwa ne , dukkan aikin dan adam  na shi ne  sai azumi to shi na Allah ne zai sakanya game da shi , to duk wanda zai iya  a cikin ku ya azumci azumi shida a shauwal  to lallai hakan na daga cikin sunna  kuma aiki ne na musdafa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
An karbo dga Abu ayubal Ansari Allah ya kara yarda a gare shi ya ce  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbataa agare shi ya ce :-(Duk wanda ya yi azumin ramadana  sannan ya bi da guda shida  a shauwal  zai kasance kamar ya yi azumi na shekara ne )Muslim ne ya rawaito
Sabo da kyakkyawa guda na da lada goma kamarta,to ramadana na da ladan wata goma, guda shidan kuma ladan wata biyu, kuma adadin watanni a gurin Allah goma sha biyu ne,
Ba laifi mutum ya yi azumin a jere ko a rarrabe, muddin dai a cikin watan shauwal ne, tamkar tana matsayin sunnoni ne na ratibi game da sallolin farilla,tana cike gurbin tawaya ne da aka samu a farilla.

        YA KU MUSULMAI :
Ku ji tsoron Allah,iya iyawanku,ku yi riko da addininku,ku kankame sunnar Annabinku, ku kuma gyara tsakaninku,ku kiyaye hadin kanku, da garinku, ku zama hanu guda kan abokin gabanku, ku roki Allah da ya tabbatar da ku ya datar da ku,
Bayan haka YA KU MUSULMAI :
Lallai abin da masu ketare iyaka suka suka aikata na harbi kan 'yan kasa da mazauna, da tsorata amintattu, da zubar da jinin wanda bai ci ba bai sha ba.da yara da mata, da keta alfarman wurare masu tsarki manya da gari mai alfarma, na daga cikin manyan laifuka abin ki ga dukkan addinai, kuma yana cin karo da ginshikai na musulunci, Alla maida musu sharrinsu a kan su.ya sanya yakinsu a tsakaninsu, kuma ya yanke karshensu.
Ya Allah ka kare wannan kasa da kariyarka.