الأحد، 30 يونيو 2019

kuma abin da ya ke a gare ku na ni'ima to daga Allah ne


Hudubar Masllacin Annabi na shaikh Abdulbari Bin Awad Assubaiti 25/10/1440Ah 28/6/2019Ac
Ni'imomin Allah ga bayinSa suna da yawa ba za'a iya iyakance su ba,mai dunbin yawa ne da ba za a iya kwalkwale su ba, suna bibiyan juna basu karewa :Allah Madaukakin Sarki ya ce : (Allah ne wanda ya halicci sammai da kasa, kuma ya saukar da ruwa daga sama sa'anan ya fitar game da shi daga 'ya'yan itace, arziki  domin ku, kuma ya hore jirgin ruwa yayi gudu a cikin teku da umarninSa, kuma ya hore muku koguna.kuma ya hore muku rana da wata suna madawwama biyu, kuma ya hore muku dare da wuni. Kuma ya baku dukkan abin da ku ka roke shi, kuma idan kun kidaya ni'imar Allah ba za ku lissafe ta ba, lalle ne mutum hakika mai yawan zalunci ne mai yawan kafurci ).
Samuwan abubuwa masu amfani da tunkude  cutarwa da ma dukkan alheri da bawa yake samu ni'ima ce daga Allah zuwa gare shi ; na ilimi da imani da aiki da zuriya da masauki da abin hawa da walwala da nasara Allah Madaukakin sarki ya ce (kuma abin da ya ke a gare ku na ni'ima to daga Allah ne) kuma lura da abin da ya ke kewaye da mu yana kaimu ga jin niimar Allah , Allah madaukakin sarki ya ce (To mutum ya duba zuwa ga abincinsa) kuma ya ce (To mutum ya duba daga me aka halicce shi).
Muminai na dubi ga ni'imar Allah na ciki da na waje: hakan sai ya kara musu imani ya kusanto da su ga Ubangijinsu suna masu ikirari da baiwarsa da alherinSa da falalarSa a gare su, Allah madukakin sarki ya ce : (suna yin gori gare ka don sun musulunta, kace kada ku yi gorin kun musulunta a kai na, Aa Allah ne ke yi muku gori domin ya shiryar da ku ga imani, idan kun kasance masu gaskiya.)
Mumini da kaifin hankalinsa da nunan tunaninsa; na dubi ga ni'imomin Allah da ke kewaye da shi, Allah madaukakin sarki ya ce yana mai sifanta halin muminin da zai karbi aikinsa : (Har a lokacin da ya kai ga mafi karfinsa,kuma ya kai shekara arba'in yace ya Ubangiji na! ka kange ni, domin in godewa ni'imarka, wadda ka ni'imta a kaina, da kuma a kan mahaifa na biyu, kuma domin in aikata aikin kwarai, wanda ka ke yarda da shi)
 Idan zuciyar bawa ta cika da imani; ni'ima ta godiya ga ni'imar sai ta tabbatu a gare shi, sai kai komonsa  su gyaru halayensa su tsarkaka,sai ya yi dace, Allah madaukakin sarki ya ce yana mai gori ga bayinSa: (kuma Allah ya soyar da imani a gare ku, kuma ya kawata shi a cikin zukatanku, kuma ya kyamatar da kafirci da fasikanci da sabo zuwa gare ku, wadannan sune shiryayyu. Bisa ga Falala daga Allah da ni'ima, kuma Allah Masani ne Mai hikima).

Ikirari da ni'imar Allah na daga cikin abin da ke hukunta tuna ni'imomin Allah, da kuma jingina su ga wanda ya bada su - daukaka ya tabbata a gare shi,- wanda ke dakon ni'imomi to ba zai gushe ba yana tuna mai bada su, wanda shi ne Allah Madaukaki  Mai ni'imtarwa da dukkan ni'imomi wadanda muke jujjuyawa a cikinta,
Yin ikirari da ni'imar Allah shine mabudin dukkan Alheri, zai sanya harshen mumini yana furta (Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Ubangijin talikai. Mai mulki ranar sakayya)  a tsawon wuninsa da darensa.
Idan musulmi ya tabbatar da ni'imar Allah a kan sa, ya yi ikirari da falolin UbangijinSa da ke kewaye da shi,; to lalle zai yi amfani da wadannan ni'imomin wurin neman yardar Allah Madaukaki, ga Annabi Sulaiman Amincin Allah ya tabbata a gare shi yana rokon UbangijinSa; (ya Ubangiji ka cusa mini in gode wa ni'imarka, wadda ka ni'imta ta a gare ni, da kuma ga mahaifana biyu, kuma in aikata aiki na kwarai, wanda kake yarda da shi, kuma ka shigar da ni sabo da rahamarka a cikin bayinka salihai,)
Ga Annabi musa abokin maganar Allah yana kulla alkawari ga Ubangijinsa     ; ( Yace Ya Ubangiji! Domin abin da ka ni'imta shi a kai na saboda haka ba zan kasance mai taimako ga masu laifi ba)
Idan musulmi ya tabbatar da ni'imar Allah a kan sa, to zai bayyana wadannan ni'imomin ne halin yana mai godiya da yabo, ba yana mai alfahari da girman kai ba, Allah madukakin sarki ya ce:    (kuma amma ni'imar Ubangijinka sai ka fada (domin godiya). Wato ka labarta wa mutane abin da Allah ya ma na ni'ima kana mai girmama wa ga Mai ni'imtarwan.
Ya zo a hadisi ( Idan Allah ya yi ni'ima ga bawa to yana so ya ga gurbin ni'iman a gare shi).Baihaki ya rawaito da isnadi hasan.
An karbo daga Abul Ahwas Aufu dan malik dan Nadlah daga Babansa yace :( Na zo ga Manzon Allah a halin ina wani yanayi na tufafi mara fasali, sai ya ce : kana da dukiya? Sai na ce :E, sai yace daga wani irin dukiya? Sai na ce : daga dukkan nau'i Allah ya bani; na daga rakuma da bayi da dabbobi, sai yace : To idan Allah ya baka dukiya ta aga hakan tare da kai).Ibnu Hibban ya rawaito a sahihinsa
  Idan ni'imomi sun tattaru ga rayuwar bawa ;to fa wani albishir ne na alheri ga ma'abocinsu muddin ya fahimci hakkinsu da ke kan shi kuma ya sauke wajibi, kuma ya sarrafa su ta hanyar da ke nuna godiya da bauta ga Allah.Amma wanda ya rudu da kansa ya yi jiji da kai da abin da Allah ya bashi na ni'ima har ma ya jinginta ta ga kansa kamar yadda Allah ya ambata a kur'ani bisa harshen Fir'auna yayin da ya ke cewa : (kuma Fir'auna ya yi kira a cikin mutanensa, yace : ya mutane na! ashe mulkin masar ba a gare ni yake ba? Kuma wadannan koguna suna gudana daga karkashi na? ashe ba ku gani ba)
 Haka ma Karuna yace( An bani shi akan wani ilimi wanda yake gare ni kawai)
To irin wannan ni'imar ce take juyawa azaba alherinta ya zama sharri samunta ya zama bala'i.
Mafi girman godiya ita ce gaggauta wa zuwa ga ibada Allah yace (A'a Allah kadai zaka bauta wa kuma kasance cikin masu godiya).
To kuma idan bawa ya yi kokari wurin bautawa Ubangijinsa yana mai godiya a gare shi bisa ni'imominsa, to lallai sakayyarsa a gurin Allah na daga cikin irin aikin da ya yi. Allah Madaukakin sarki ya ce : (Lalle wannan ya kasance sakayya a gare ku, lalle aikin ku ya kasance abin godewa).
Bawa ba zai iya sauke nauyin godiyan ni'immomi ba duk yadda ya yi kokari , ya isan mishi ya yi kokari ya samu yardan Allah Madaukaki! Ya samu ya yi godiya na gabadaya da godiya na musamman, a duk lokacin da ni'ima ta sake samuwa sai ya sake mata sabuwar godiya. Ya zo a hadisi Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce (wanda ya ce idan ya wayi gari; Ya Allah abin da ya wayi gari da ni na ni'ima ko wani daga cikin halittunka to daga gareka ne yake kai kadanka baka da abokin tarayya kuma dukkan yabo da godiya naka ne to hakika ya sauke nauyin godiya na wannan rana, wanda ya ce idan ya yi yammaci Ya Allah duk abin da ya yi yammaci da ni na ni'ima ko daya daga cikin halittunka to daga gareka yake kai kadanka baka da abokin tarayya, to yabo da godiya ya tabbata agreka to hakika ya sauke nauyin godiya na wannan dare).
kuma  (An karbo daga Rifaa dan Rafi' Azzuraki ya ce mun kasance wata rana muna salla a bayan Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya yin da ya daga kansa daga ruku'u kuma ya ce :Allah ya amsa ga wadanda suka gode mishi sai wani mutum a bayan shi ya ce:Ubangijinmu godiya ta tabbata gareka ,godiya mai yawa tsarkakakkiya mai albarka a cikinta yayinda Manzon Allah ya idar da sallah sai ya ce: wanene yayi magana dazu? sai wanan mutumi ya ce nine ya manzon Allah! sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce hakika naga mala'iku talatin da dori suna rige rige waye zai fara rubuta ta )Hakim ne ya rawaito da ibnu hibba da isnadi ingantacce
 Musulmi zai yi gaggawa zuwa kofan adu'a yana rokon Ubangijinsa da ya mishi ilhama na godiya, domin ya kankare tawaya da nakasa, ababin niimomi (kuma ka samu masu godiya bisa niimarka masu kuma kyawtata yabo da ita agare ka to ka karbe ta ka cikata agare mu )Ibnu Hibban ne ya rawaito.
Amma wanda idonsa ya makance daga ganin ni'imomin Allah to hakika wannan ya fada  rabon shaidan da waswasinsa da makircinsa, kura'ani ya hakaito hakan daga gare shi (saannan zan zo musu daga gaba garesu kuma daga baya garesu kuma daga damansu da kuma hagunsu ba za ka samu mafiya yawansu ba suna masu godiya)
Musulmi na gafala daga riskan ni'imomin Allah a gare shi yana mai   rainata ma a lokacin da ya ga abin da ke hanun wasu na ni'imomi. A cikin sahihu muslim daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(ku yi dubi zuwa ga na kasa da ku kar kuyi dubi zuwa ga wanda ya ke sama da ku domin haka ya fi dacewa don kar ku rena niimar Allah a gare ku.
Na daga cikin munanta ladabi ga  Allah dulmuya cikin ni'imomi da manta Mai yin ni'imar da kuma zurfafa wa cikin farin ciki da manta Mai yaye bakin ciki  da bacin rai, Allah Madaukakin sarki ya ce (kamar wancan ne Allah ya ke cika niimarsa a kanku tsammaninku kuna mika wuya )
(To idan sun juya to abin da ya wajaba a kanka shi ne isarwa bayyananniya) (suna sanin niimar Allah sa'annan kuma suna musantawa kuma mafi yawansu kafirai ne )kuma ya ce: (kuma wanda ya musanya niimar Allah bayan ta zo mishi to lalle ne Allah mai tsananin ukuba ne).
                 
                           Huduba ta biyu
 Mai hankali ya na kiyaye amfani da  ni'imomin Allah ba tare da ya yi sakaci da hakkin Allah a ciki ba  da bauta da godiya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Idan ka ga Allah yana baiwa bawa abin da ya ke so alhali shi kuma bawan yana saba mishi to lalle hakan a gareshi daurin talala ne sannan sai aka yayeta da wannan ayan(saannan kuma A lokacin da suka manta abin da aka tunatar da su da shi sai muka bude a kansu kofofin dukkan kome har a lokacin da suka yi farinciki da abin da aka basu, muka kama su kwasam, sai gasu sun yi tsuru- tsuru, sai aka katse karshen mutanen,wadan da suka yi zalunci, kuma godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai ) Ahmad da Baihaki ne suka rawaito Albani ya inganta shi.

Kuma musulmi na sanya bautarsa a hade da abin da ya ke riska na ni'ima, idan an bashi ni'ima sai ya yarda in an dauke sai ya yi fushi, to wannan sifa ce abin zargi,
 Allah Madaukakin sarki ya ce (kuma cikin mutane akwai mai bauta wa Allah bisa gefe, sa'annan idan wani alheri ya same shi sai ya natsu da shi, kuma idan wata fitina ta same shi sai ya juya baya akan fuskarsa ya yi hasarar duniya da lahira.
An karbo daga Abdullahi dan Abbas Allah kara yarda a gare su, yace: (kuma cikin mutane akwai mai bauta wa Allah bisa gefe,) Mutum ne zai zo Madina idan matarsa ta haifi da dokin sa ya haihu sai ya ce : wannan Addini ne mai kyau, idan matarsa bata haihu ba dokin sa bai haihu ba sai ya ce : wannan mummunan addini ne).

الجمعة، 21 يونيو 2019

kofofin tuba


Hudubar Masllacin Annabi na 11-10 -1440AH/14-6-2019 AD na Sheikh Abdullah bin Abdurrahman Albu'aijan.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, muna gode masa muna neman taimakonsa muna neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi duk wanda ya batar da shi ba zaka sama mishi majibinci mai shiryarwa ba.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, ya halitta kuma ya daidaita abin halitta ya kaddara (abin da ya so) ya shiryar, na shaida Annabi Muhammad bawansa ne kuma manzon sa ne, wanda ya turo shi da gaskiya da shiriya, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabbansa da duk wanda ya bi sawun shi,ya bi tafarkinsa da kyautatawa har zuwa ranar sakayya,
Bayan haka: Lallai mafi alherin zance shi ne littafin Allah, kuma mafi alherin shiryarwa shine shiryarwa Muhammad dan Abdullah, Mafi sharrin al'amura sune fararrunta, dukkan fararrun abubuwa bidiah ne, dukkan bidiah bata ne dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah … ku ji tsoron Allah cikin abin da ya umarta, ku hanu daga abin da ya hana ya tsawatar, ku sani dukkan karami da babba ana rubuta shi, (ya ku wadanda suka yi mani ku bi Allah da takawa, kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma ku bi Allah da takawa lalle Allah mai kididdigewa ne ga abin da ku ke aikatawa,)
Ya ku bayin bayin Allah!
Lokaci na albarka da falala da alheri da da'a ranakunsa ya kare an nade ayyukansa, lalle wata ne mai girman falala, tasirin sa a cikin Al'uma na da ban mamaki, masu nasara cikin shi sun ribata,masu kokari cikinsa sun samu ganima,ina ma da mun san wanda aka karbi ayyukansa mu mishi barka! Wane ne baa karba mishi ba mu jajanta mishi,
Madalla da farincikin wanda suka rabauta, Allah ya musu ilhamar tuba, ya datar da su ga biyayya, muna roka musu Allah da ya karba musu ya dora su kan daidai.
Ya  kaiton hasarar wadanda suka rasa wannan alheri aka katange  su daga Ubangijin su, damammaki a rayuwa suka kwace musu.ga lokutan alheri basu ribaci komai ba sai hasara da nadama,
Sai dai ya jama'ar musulmi ! kofofin tuba basu gushe ba suna bude ba a rufe su ba bayan watan ramadan,Ubangijinmu mabuwayi da daukaka yana karbar tuba daga bayin sa a kowane zamani da guri  (Shi ne yake karbar tuba daga bayin sa kuma yana yafe munana, kuma ya san abin da kuke aikatawa).
     Ya tabbata daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace :Lalle Allah ya fi farinciki   da tuban bawansa mumini  akan mutumin da  yake cikin kasa ta sahara wacce  ke da ababan halakarwa   yana tare da dabbarsa  abin cin shi da abin shan sa na kanta   sai ya yi bacci , da ya farka sai ya ga ta tafi  ya yi ta nemanta  har sai da  kishi ya cimmasa  sai ya ce bari na koma wurina da na kasance a cikin shi  sai na je na yi bacci har ma na mutu  sai ya dora kanshi  a bisa damtsen shi don ya mutu yana halin haka  sai ga dabbarsa a kan sa  tare da ita ga guzurin shi da abin cin shi  da abin shan sa  sai  ya rike linzamin ta yayi kuskure don tsananin farin ciki yana mai cewa ya Allah kai ne bawana ni ne Ubangijin ka  .
An karbo daga Abu Huraira  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agare shi ya ce:(Idan wani yanki na dare ya shude ko kuma wani sulusin  shi , Ubangijin mu mai tsarki da daukaka zai sauko  zuwa ga  sama na  duniya  sai ya ce:-
Ko shin akwai mai tambaya na ba shi , ko shin akwai mai roko na amsa mishi , shin akwai mai neman gafara a gafarta masa har gari ya waye  . Muslim ne ya rawaito)
Zuwa ga wanda daman ramadan ya kwace mishi  to ka yi gaggawa zuwa ga tuba  kafin lokaci ya tsere   da kuma shammatan ajali kada ka yanke tsammani don duk dan adam mai kuskure ne  abin zargi  na ga wanda ya doge  kuma alhali yana da Ubangiji mai gafarta zunubai kuma bai nemi gafarar sa ba , ba don kun kasance kuna kusakurai ba kuma kuna neman gafara da  Allah ya tafiyar da ku ya kawo wasu mutane wadan da suna kuskure kuma suna neman gafara sai Allah ya gafarta musu .
YA KU BAYIN ALLAH:
Ku ji tsoron Allah kuma ku nemi gafarar sa  kuma ku koma zuwa gare shi ku mar da'a  kada ku jinkirta tuba domin  mutuwa na zuwa bagtatan  .
Allah madaukakin sarki ya ce :-(Ku tuba suwa ga Allah gaba dayanku ya ku muminai  ko za ku  rabauta)
Kuma ya ce :-( Ka ce  ya ku bayi na wadanda suka   barnatawa kawunan su  kada ku yanke tsammani daga rahamar Allah lallai Allah yana gafarta zunubai baki daya  lallai shi mai gafara ne kuma mai jin kai .  Ku koma zuwa  ga Ubangijinku  ku mika wuya gare shi  kafin azaba ya zo muku  sa'annan ba za a taimaka muku ba , ku bi mafi kyaun  abin da aka saukar gare ku daga Ubangijin ku  tun kafin azaba ya zo muku  bagtatan a halin kuna baku sani ba  kada rayi ta ce  ya hasara ta  bisa  abin da na yi sakaci a janibin Allah  , ko da na kasance cikin  wadan da suke masu isgili  ko kuma ta ce ina ma da Allah ya shirye ni  da na  kasance cikin masu takawa  , ko kuma ta ce ya yin da ta ga azaba  ina ma da ina da kome da na kasance cikin masu kyautatawa 

YA KU MUSULMAI:
Lallai ibada na da tasiri  cikin halayen ma'abocinta Allah madaukakin sarkiya ce :-(Lallai sallah na hani ga alfasha  da munkari)
Na daga cikin alamomin karban ayyuka  akwai canzawan halayen zuwa mafi kyan hali  a daya bangaren kuma  yana daga cikin alamomi na  rasa alheri da rashin karban aiki  akwai komawa baya  daga da'a  bayan shudewan ramadana  yanayin halaye ya canza zuwa mafi muni  domin sabo sashi na janyo sashi , madalla da kakkyawa bayan mummuna  sai ta goge ta  mafi kyaunta kuma shi ne kyakkyawa bayan kyakkyawa  tana mai binta , ku roki Allah tabbatuwa akan da'a har zuwa mutuwa  kuma ku nemi tsarin Allah  daga juyawar zukata  haka nan kuma daga warwarewa bayan daurewa .

 Abin mamaki da munin  kaskanci  na sabo  bayan izza ta da'a  tir da  talauci na  kwadayi bayan wadatuwa da wadatan zuci  ku roki Allah tabbatuwa , ya tabbata daga Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Lallai dayanku  zai yi aiki irin na 'yan aljanna  har sai ya kasance tsakanin shi da ita  face zira'I  sai littafin sa ya rigaya  , sai ya yi aiki irin na 'yan wuta sai ya shige ta ,  kuma lallai dayan ku zai yi aiki irin na 'yan wuta   har sai ya kasance tsakanin shi da ita face zira'I sai littafin shi ya rigaya sai ya shigeta  Buhari ne ya rawaito)
Ina fadin abin da kuke ji ……….

HADUBA TA BIYU

Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga Allah wanda  yake karban tuba daga bayin sa  kuma yake yafe kusakurai kuma ya san abin da kuke aikatawa ,  kuma yana amsa kiran wadan da suka yi imani kuma  suka yi aiki na kwarai   kuma yana kara musu daga falalar sa .
 YA KU MUSULMAI :
Watanni dukan su lokuta ne na ibada  ko da sun sha banban  sun saba a wurin fifiko  da ayyuka  rayuwa dukkanta   dama ce ta aiki  da biyayya   ko wanne yana wayan gari yana mai saida kan sa akwai mai 'yantata akwai kuma mai halakata ,  kuma kowa ana yassare mi shi abin da aka halicce shi  akanta   , .
To ku sabarwa kawunan da da'a ku nemi taimako game da ita da tuba  da neman gafara  da komawa zuwa gare shi da marairaicewa  da kuma murakaban Allah  guda mai rinjayi  a sirri kuma da bayyane a dare da wuni .
 (Ku bar  sabo na zahiri da na badinin  sa  lallai wadanda suke aikata laifi za a sakanya musu da abinda suka kasance suna aikatawa)
YA KU BAYIN ALLAH:
Ku rantawa Allah rance kyakkyawa , ku kaddamarwa kawunan ku abu mai amfani , (Duk wani abu da za ku kaddamar wa kawunan ku na alheri za ku same shi a wurin Allah).
(Wane ne zai rantawa Allah rance mai kyau sai ya ribanya mishi ribanyawa mai yawa).
Sannan ku sani cewa azumi garkuwa ne , dukkan aikin dan adam  na shi ne  sai azumi to shi na Allah ne zai sakanya game da shi , to duk wanda zai iya  a cikin ku ya azumci azumi shida a shauwal  to lallai hakan na daga cikin sunna  kuma aiki ne na musdafa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
An karbo dga Abu ayubal Ansari Allah ya kara yarda a gare shi ya ce  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbataa agare shi ya ce :-(Duk wanda ya yi azumin ramadana  sannan ya bi da guda shida  a shauwal  zai kasance kamar ya yi azumi na shekara ne )Muslim ne ya rawaito
Sabo da kyakkyawa guda na da lada goma kamarta,to ramadana na da ladan wata goma, guda shidan kuma ladan wata biyu, kuma adadin watanni a gurin Allah goma sha biyu ne,
Ba laifi mutum ya yi azumin a jere ko a rarrabe, muddin dai a cikin watan shauwal ne, tamkar tana matsayin sunnoni ne na ratibi game da sallolin farilla,tana cike gurbin tawaya ne da aka samu a farilla.

        YA KU MUSULMAI :
Ku ji tsoron Allah,iya iyawanku,ku yi riko da addininku,ku kankame sunnar Annabinku, ku kuma gyara tsakaninku,ku kiyaye hadin kanku, da garinku, ku zama hanu guda kan abokin gabanku, ku roki Allah da ya tabbatar da ku ya datar da ku,
Bayan haka YA KU MUSULMAI :
Lallai abin da masu ketare iyaka suka suka aikata na harbi kan 'yan kasa da mazauna, da tsorata amintattu, da zubar da jinin wanda bai ci ba bai sha ba.da yara da mata, da keta alfarman wurare masu tsarki manya da gari mai alfarma, na daga cikin manyan laifuka abin ki ga dukkan addinai, kuma yana cin karo da ginshikai na musulunci, Alla maida musu sharrinsu a kan su.ya sanya yakinsu a tsakaninsu, kuma ya yanke karshensu.
Ya Allah ka kare wannan kasa da kariyarka.

الجمعة، 17 مايو 2019

ka yi sujada ka kusanto


Hudubar Masllacin Annabi na sheikh Abdulbari Bin Awad Assubaiti 12 Ramadan 1440Ah
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, tsira da amincin Allah su tabbata ga  mafificin halittun Allah,
Bayan haka !
A kalmomi biyu na karshen farkon sura da aka saukar a Alkur'ani Allah yana cewa:(Kuma ka yi kujada ka kusanto ) an karbo daga  Abu Huraira  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( lokacin da bawa ya fi kusanci da Ubangijin shi shi ne a halin yana sujjada , to ku yawaita adu'a ) Muslim ne ya rawaito
Sujada shi ne mafi daukakan hali na bawa , a cikin shi ne mutum zai ji dadin rusunawa mabuwayi mai girma  da kuma  kawa irin na kankan da kai ga mai rahama mai jin kai , wasu lokuta ne na karamci da albarka  wanda ba su da iyaka .
 Acikin sujada ne a ke jin dadin da baya misaltuwa   da yaye walwalan zuciya  wanda ba alkalamin da zai iya iyakance shi  yana  kaurar da musulmi daga kunci ,  zuwa ga yalwa mai fadi  na kasa  cikin sararin samaniya  sabo da haka ne  (Aisha Allah ya kara yarda a gare ta  ta sifanta tsayuwan daren Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da cewa; yana sujjada  guda da zai kai dayan ku ya karanta aya hamsin  kafin ya dago)  Buhari ne ya rawaito .
Sujada na kara wani haske na imani   daga ma'abocin shi ya jefa wani walwala a zuciya da natsuwa  ya bashi wani  gairmamawa , Allah madaukakin sarki ya ce :-(Muhammadu Manzon Allah ne , kuma  wadan da suke tare da shi  suna masu  tsanani ga kafurai  masu tausayi a junan su  za ka gansu suna masu yawan ruku'u da sujada  suna neman falala daga wurin Allah  da yarda  alamun su  na fiskan su na gurbin sujada )
Asujada ne Ubangiji ke kasancewa kusa da wanda ya roke shi  , Ubangiji mai tsarki    yana kusa da wanda ya roke shi  , mai amsawa ne ga wanda ya nemi ganawa da shi   mai badawa ne ga wanda yayi fata gare shi  duk wanda ya kusanci Allah to lallai zai riski kyauta mafi yalwa daga Ubangijin shi, kuma ya samu matsayi mafi
aminci da yakini da kariya mai karfi  ,  Allah madaukakin sarki ya ce (To amma (  idan mai mutuwan ya kasance daga makusanta   sai hutawa  da kyakkyawan abinci da aljanna mai ni'ima )
Makusantan suna da Rauhun shi ne;  hutu  da natsuwa da farin ciki  da kuma annashawa , Raihan   shi ne suna da ya tattaro dukkan  wani jin dadi na  jiki  na daga abinci ne ko abin sha  da makamantan su ,  da  (aljanna mai ni'ima) wanda a cikin ta akwai abinda ido bai gani ba kuma kunne bai ji ba kuma bai halarto a tunanin wani dan adam  ba yana yiwa makusantan shi albishir yayin  halartowan mutuwan su da wannan albishir din  wanda  rayuka ke kusa da su fire sabo da tsabar jin dadi da farin jiki , (ka yi sujada kuma ka kusanto )      
A ko wani sujada kana da daukaka na daraja   da kusanci na matsayi  da kuma kusanci na wuri  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (Ba wani bawa da zai yi sujada  don Allah face an rubuta mishi kyakkyawa da ita , an kankare mishi mummuna da ita  an kuma daga darajar ku da  ita  , to ku yawaita yin sujada ) Ibn Maja ne ya rawaito da isnadi ingantacce
To kyautan Allah bai  karewa duk wanda ya kusance shi sai ya saukar da shi bisa falalan sa daraja irin na Annabawa  da siddikai da shahidai  da salihai , Manzon Allah tsira  da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce da Rabi'ata Dan Ka'ab Al-Aslami a lokacin da ya nemi kusanci da Manzon Allah a aljanna  sai  ya ce da shi:-(  ka taimaka mini akan kanka da yawan sujada)   Muslim ne ya rawaito

     (ka yi sujada kuma ka kusanto ) a cikin sujada ne alamomi na gaskatawa da imani ke bayyana alamomin yakini da mika wuya ke fitowa fili , an karbo daga Aliyu dan Abi Dalib  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :-  ya kasancen  daga  cikin adu'o'in manzon Allah  tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi a sujadan sa  Allahumma laka sajadtu , Aya Allah don kai na yi sujada , wabika amantu , da kai ne kuma na yi imani  wa laka aslamtu, kuma da kai na mika wuya  ,  fiska ta ta yi sujada ga wanda ya halicce ta ya sauwara ta  ya tsagi jinta da ganin ta  tsarki ya tabbata ga Allah mafi kyaun masu halitta )Muslim ne ya rawaito
(ka yi sujada kuma ka kusanto ) lalle sujada na    cikin ibada  wanda dukkan halitu suka yi tarayya suka tattaru a kanta (Kuma ga Allah abinda yake cikin sammai da kasa na dabba da mala'iku suke yin sujada , kuma basu kangara .  Suna tsoron Ubangijin su daga bisan su  kuma  suna aikata abinda ake umarnin su )
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce ni ina ganin abinda bakwa gani kuma ina jin abinda bakwa ji , sama ta yi  kara kuma ta cancanci ta yi karan sabo da  babu wani bigirea na yatsu fa ce mala'ika yana daure da fiffigen shi yana mai sujada ga Allah , wallahi da kunsan  abinda na sani da kunyi dariya dan kadan kunyi kuka mai yawa . Da ba ku ji dadi da mata ba akan shimfidi  da kun fita kwararo –kwararo  kun yi kururuwa  kuna kara  zuwa ga Allah ) Nasa'I da Ibn Maja ne suka rawaito  da Ahmada.
1.   (ka yi sujada kuma ka kusanto ) ka yi sujada kana mai rokon Ubangijin ka kana mai kiran mahaliccin ka  , kana mai kankan da kai zuwa ga masoyin ka , kai din nan kana aljanna ne daga cikin aljannoni na duniya , ka yi sujada sujudan mai tsoron Allah   a duk lokacin da ka ji ayoyin alkur'ani , bayanansa suka ratsa ma zuciya.

 Allah madaukakin sarki yana cewa (Kuma yana abun karatu  mun rarraba shi domin ka karanta shi ga mutane akan jinkiri,  kuma mun sasaukar da shi sassaukarwa  ka ce ku yi imani da shi ko kuwa  kada  ku yi imani ,   lalle ne  wadan da  aka  baiwa  ilimi  gabaninsa  idan ana  karatun sa  akan  su   suna   faduwa   ga habobin  su  suna masu sujada )
(Kuma suna cewa tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu lallae ne wa'adin Ubangijin mu ya kasance hakika abin aikatawa , kuma suna faduwa ga habobin su  suna  kuka  kuma  yana  kara  musu  tsoro  )
(ka yi sujada kuma ka kusanto ) kuma duk lokacin da ka tuna jinkirin ayukan ka kuma ka ji zafin zunuban ka da gafalar ka  ka rinka kwankwasa kofar tuba da neman gafarar ka  to Allah  madaukaki yana cewa  yana mai siffanta Annabin sa Dauda  Amincin Allah ya tabbata a gare shi
(Dauda ya tabbatar da cewa mun fitine shi ne, sabo da haka,  ya nemi Ubangijin sa gafara  kuma ya fadi yana mai sujada  kuma ya mayar da al'amari ga Allah , sabo da haka muka gafarta masa wancan .  Kuma lallai yana da wata  kusantar daraja a wurin mu da kyawun makoma )
(ka yi sujada kuma ka kusanto ) Idan bakin ciki ya tananta a gare ka , matsaltsalu sun kyawaye ka   ga fitintinu sun dame ka , to lalle sujada  yayewa ne ga dukkan wani bakin ciki   duk wanda zuciyar sa  ya kuntata   mutane suka bata mishi rai to, ya yawaita salla da sujada da adu'a   Allah madaukakin sarki ya ce :- ( Hakika mun sani cewa  zuciyan ka na kuntata   sakamakon abinda suke  fadi to ka yi  tasbihi da godiy a ga Ubangijin ka  ka kasance cikin masu sujada  )
 Sujada na kashe fushin Uabangiji mai rahama kuma  yana  haifar da yardan sa  tsarki ya tabbata ga Allah  madaukaki :- Ya zo a sahihi ingantacce  na Annabi tsira da aminci su tabbata a gare shi (kan cewa idan mutane sun tsaya a farfajiyan ranar alkiyama  aka tafi neman  ceto   wurin Annabawa, har suka kai ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi,sai suka ce ya Muhammad ba ka ga halin da muke ciki ba? Ba ka ga musibar da ta same mu ba? Sai yace "Da ma neman ceton tawa ce" sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya tafi ya yi sujada a karkashin Al'arshi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yace : sai na nemi izinin Ubangiji na sai ya ban izini,shi na gode mi shi,da wasu yabo da ba zan iya su yanzu ba, wanda Allah zai min ilhamar su, sai na fadi ina mai sujada sai a ce ya Muhammad daga kanka, ka fada za a saurare ka, ka roka zaa baka, ka nemi ceto za a baka.) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Sai Allah ya sanya sujada a matsayin ceto kuma tsani don fita daga azabar matattarar kiyama.
A duk lokacin da ka samu wasu alheri da kyauta mai yawa daga Mai rahama to ka fadi ka yi sujada ga  Allah    don godiya  bisa ni'imarsa.
An karbo daga Abu bakrata yace a duk lokacin wani abu na farin ciki ya samu Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, sai ya fadi ya yi sujada ga Allah)Su biyar suka rawaito banda Nasa'i
An karbo daga Abdurrahman Bin Auf  Allah ya kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya yi sujada sai ya tsawaita sujadan sannan sai ya daga kansa sai ya ce " Lalle Jibrilu ne ya zo ya mini albishir sai na yi sujada don godiya ga Allah" Ahmad ne ya rawaito Hakim kuma ya inganta shi.

Huduba ta biyu
Bayan haka!
Mamakin da kyaun sauyawan mutumin da zai kwankwadi dadin sujada a dararrakin ramadana da falalarsa,Allah Madaukakin sarkin yace :(Daga wani sashe na dare ka yi masa sujada kuma ka masa tasbihi dare mai tsawo,)   
Allah Madaukakin sarkin yace :(Da wadanda suke kwana suna sujada da tsayuwan dare) Allah Madaukakin sarkin yace (Shin wanda yake mai tawaliu tsawon dare  yana mai sujada ku yana mai tsayuwa ga sallah yana tsoron lahira kuma yana fatan rahamar Ubangijinsa(yana daidai da waninsa?)
Ya kai mai tsere zuwa ga aikin alheri a ramadan, ka yi gaggawa  a tafiyarka zuwa ga ubangijinka.
Hasara dukkan hasara shine a haramtawa bawa ni'imar sujada gaba ga Ubangiji.
Idan dan'adam ya karanta sajada sai yayi sujada sai shaidan, sai shaidan  ya kebe yana kuka yana cewa : ya bonenSa- A riwayar Abu kuraib "ya bone na"
An umarci dan Adam da sujada sai yayi to yana da Aljanna.
An umarce ni da sujada sai na ki to gashi zan shiga wanda) Muslim ne ya rawaito
Duk wanda ya yi girman kai bai yiwa Ubangiji sujada  ba a duniya ba, to ba  zai   iya yin haka a lahira ba in an kiraye shi da haka.
An karbo daga Ada'u dan yasar daga Abu Said Allah ya kara yarda a gare shi yace  :Na ji  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:UbangijinMu zai yaye kwabrinsa sai dukkan wani Mumini da mumina, su yi sujada  sai yasaura kawai wanda ya kasance mai yin sujada don riya da neman a ji. Sai ya je don yayi sujada sai bayansa ya zamza  shinfida guda).Bukhari ne ya rawaito


  



الجمعة، 3 مايو 2019

Ayyukan Biyayya a Watan Ramadan


Hudubar Masallacin Annabi 28-8-1440AH Sheikh Abdulmuhsin Alkasim
Hudubar Farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode masa kuma muna neman taimakonsa da gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi, kuma duk wanda ya batar babu mai shiryar da shi, Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah,shi kadai yake ba shi da abokin tarayya, na kuma shaida Annabinmu Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata gare shi da iyalansa da sahabbansa da aminci tabbatacciya mai yawa.
Bayan haka,
 ku ji tsoron Allah yadda ya dace a ji tsoron shi, ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci.
Ya ku Musulmai!
Ranaku da dararraki na ta tafiya da sauri,ga shekara na kokarin nade tabarmarsa da gaggawa,.bayi na tafiya zuwa ga Allah ! kuma su riski ayyukansa.
Na daga falalar Allah da karamcinsa ya zaba mana wasu lokuta na da'a, ya zabi wasu ranaku da dararraki da wasu sa'o'i, domin kwadayin rahamar Allah ya yawaita a samu karin kaimi da masu zage damtse,da gasar masu gasa cikin ayyukan alheri, a duk lokacin da jinjirin watar ramadana ya kada sai ya buso mana da wasu albarka masu yawa, sai musulmai su fiskance shi da annashawa, zukatarsu su cika da farinciki sabo da shi,ta iya yiwuwa sa'a guda da zaa riska ta daga darajan mutum ta sa Allah ya yarda da shi ya kuma samu walwala,
Ga wata mafi daraja ta dumfaro mu,lokaci ne mai girma da Allah ya kebance ta da daukakawa da girmamawa, sai ya turo manzonsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya sauke littafinsa a cikinta,ya wajabta azumtarta, sa'ointa na da albarka, lokutan cikinta ana raya su da ayyukan alheri, alheri na bibiyan juna a ciki,albarka na gamewa a ciki,lokaci ne na kyautatawa da bada sadakoki, lokaci ne na gafara da kankare laifuka, wuninta azumi darenta kuma tsayuwan dare ana nafila, ana raya ta da sallah da karatun Alkur'ani,Ana bude kofofin Aljanna,ana kulle kofofin wuta,ana daure shaidanu a cikinta, a cikinta akwai dare guda da ya fi watanni dubu, wanda ya rasa alherinta lalle ya yi hasara.
Ramadana fage ne mai fadi na gasa cikin ayyukan da'a,  kuma wani kyauta ne na tsarkake rayuka daga kazanta da laifuka,wata ne mai girma ana ribanya ayyukan Alheri, ana kankare kusakurai da laifuka, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Salloli guda biyar da juma'a zuwa juma'a da Ramadan zuwa ramadan kankara ne ga abin da ke tsakanin su muddin aka nesaci manyan zunubai)Muslim ne ya rawaito
A cikin ta musulmai ke sauke rukuni daga cikin rukunan musulunci, kuma wani abu ne na aiki bayyananne da ke nuna girman wannan addini da hadin kan musulmai, a cikinta ne fadin Allah Madaukakin sarki ke bayyana na cewa : (Lalle wannan Al'umarku ce Al'uma guda Ni kuma Ubangijinku ne to ku bauta mini).
Ribatan lokutan alheri budi ne daga Allah ga wanda ya so na daga bayinSa, a cikin Ramadan tushen ibadoji  kuma mafi girma ke haduwa ga musulmai, sallah sadarwa ne tsakanin bawa da Ubangijinsa, bata rabuwa da musulmi a dukkan rayuwarsa,sallan mutum cikin jam'I farilla ne ta fi sallarsa a gidansa da kasuwansa da lada ashirin da bakwai.
Ya dace ga musulmi da ya nemi taimako da azuminsa bisa sallarsa, kuma ya zama yana kaso mafi girma na sallah To ( wanda ya yi tsayuwan Ramadan bisa imani da neman lada zaa gafarta masa abin da ya gabata na zunubansa)Bukhari da muslim ne ya rawaito. Duk ( wanda ya yi tsayuwan dare  tare da liman har aka tashi  za a rubuta mishi cikakken tsayuwan dare ) Tirmizi ne ya rawaito.
Zakka da sadaka tsarkaka ne da habaka ga dukiya kuma  wadata ne ga zuci da tsarkaka, tasirinta a bayyane yake ga rayi da dukiya da   da, tana tunkude bala'I, tana janyo yalwa, wanda ya yi wa bayin Allah kyauta Allah zai yi masa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(Allah Mabuwayi da daukaka ya ce: Ya kai dan Adam ka ciyar zan ciyar da kai)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Dukkan mutum na karkashin inuwar sadakarsa ranar alkiyan, to ku yi sadaka ko da da dan kadan ne, ka jiyar wa kanka dadi, ka sadar da zumunci da shi ga wanda bai da shi, Duk wanda ya shayar da mai azumi to yana da kwatankwacinsa na lada, kuma na daga cikin kyautarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai ciyarwa da kuma kyauta, yana bada kyautar mutumin da bai tsoron talauci, in ya ciyar zai bada da yawa, in ya bada kyauta zai yawaita , ba ya maida mai tambaya. Baa tambayarsa wani abu ba face sai ya bada,
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance mafi kyauta a cikin azumi to shi yafi iska mai busawa.
Azumi shi ne   alami mafi girma cikin alamomin addini  a cikin wannan wata mai falala  musulmai na guzurin tsoron Allah a cikin shi,  Allah madaukakin sarki ya ce :-(Ya ku wadanda suka yi imani  an wajabta muku yin azumi kamar yanda aka wajabtawa wadanda suka gabace ku ko za ku samu tsoron Allah)
Ladan shi ba yi da kididdiga ko iyaka, Allah Madaukakin sarki ya ce a hadisin Alkudsi:  ( Dukkan aikin dan adam na shi ne sai azumi, lalle shi nawa ne kuma ni nake sakanya wa game da shi)  Buhari da Muslim ne  suka rawaito.
Kuma ( wanda ya yi azumin ramadana yana mai neman lada an gafarta mishi zunuban sa)
Azumi kan yi shamaki tsakanin ma'abocin shi da sharrace-sharrace  da laifuka  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:- ( azumi garkuwa ce   ).
Umra na daga cikin ayukan da ake riba ta a wannan wata  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- (yin umra a watan Ramadan na dai-dai da Hajji )Buhari da muslim ne suka rawaito
Kuma kur'ani maganan Allah ne madaukaki kuma hujjan sa ne kan halittun shi , kuma shi wani mabubbuga ne na hikima  , kuma aya ne na sako  babu hanya zuwa ga Allah sai ta hanyar shi   babu tsira gare mu ba tare da shi ba  haske ne  na basira  da kuma gani  wanda ya kusance shi zai samu daukaka , wanda ya yi riko da shi kuma zai samu buwaya  karanta shi lada ne da kuma shiriya , bitar sa kuma ilimi ne da tabbatuwa akan tafarki  aiki da shi kuma wani katanga ne da kuma aminci , koyar da shi kuma da kira zuwa gare shi kambi ne  akan kawunan masu da'a ,  a cikin ramadana ne kur'ani ya sauka  sabo da haka ake karfafa yawan karanta shi a cikin sa da lura da ma'anonin shi  da  koya da koyar da shi  da kuma aiki da shi da riko da koyarwar sa , Allah mabuwayi da daukaka ya ce:- (watan  ramadan wanda aka saukar da kur'rani acikinta  shiriya ne ga mutane,  kuma da bayyanannu na daga shiriya da kuma rarrabewa).
Jibrilu alaihissalatu wassalam  ya kasance yana bitar alkur'a ni da Annabin mu tsira da amincin Allah su tabbata a gare  shi  sau daya a ko wani  shekara , a shekaran da ya rasu kuma ya yi bita da shi  sau biyu  amincin Allah ya tabbata a gare shi .
Adu'a ibada ce kuma kusanci ne   wani garabasa ne ba tare da wahala ba ,  kuma riba ne da ba  tsiya tare da shi  kuma shi yana janyo yalwa , kuma makiyi ne ga dukkan wani bala'i   mutum ba zai taba halaka ba muddin yana tare da adu'a  da shi ne bawa  zai kai ga burin shi ya kuma  riski bukatar shi , sau dayawa yakan kusanto da abin da ke nesa kuma sau dayawa yakan saukake abin da ke da tsanani , sau dayawa yakan yaye bakin cikin abin da akwai bakin ciki a ciki,  kuma mafi karbuwan adu'a  shi ne wanda ya kasance a cikin  yankin karshe na dare  idan bawa ya marairaice gaba ga  Ubangijin shi to, Allah zai amsa rokon shi ,  idan rayi ta ji  yunwa sai zukata su yi taushi , mai azumi ba'a maida adu'ar sa  Ibn Rajab Allah ya kara mishi rahama ya ce :-(Mai azumi yana cikin bauta ne a daren sa da wunin sa  ana kuma amsa mi shi adu'a a azumin shi ya yin shan ruwan shi  , to, a haka shi   mai azumi ne kuma mai hakuri  a daren shi kuma yana mai ci kuma mai godiya ) .
Wanda aka yiwa dace shi ne wanda ya yawaita kwankwasa  kofar sama  ya sanyawa kanshi cikin wadannan kwanaki da dararraki   hyana mai adana .
  Ambaton Allah ibada ce mai girma kuma mai sauki  wanda ya ambaci Allah Allah zai ambace shi , bawa idan harshen shi bai shagaltu da zikiri ba to maganganu marasa amfani za su shagaltar da shi   da kuma sabonnin su .
  Addini mu'amala ne mafi dacewan halittu da kyautatawan ka shi ne wanda  Allah ya hada hakkinsa da na su ,  to iyaye biyu aljannan ka ne  kuma wutan ka  su suka fi dacewa a cikin mutane wurin kyautata mu'amala da su   , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :- ( Hancin shi ya dumbuli kasa , kuma hancin shi ya dumbuli kasa kuma hancinsa ya dumbuli kasa! Sai aka ce :wanene ya Manzon Allah? Sai yace : duk wanda ya riski iyayensa a halin girma dayansu ko dukansu biyu kuma bai shiga Aljanna ba)Muslim ne ya rawaito. kuma (Zumunci na danfare da Al'arshi yana cewa: duk wanda ya sada mini Allah zai sada mishi, wanda ya yanke min Allah zai yanke mishi, wanda zai burge shi a yalwata mi shi arzikin shi a kuma jinkirta mishi  a bayan shi to ya sada zumuncin shi .) Buhari da Muslim ne suka rawaito
 Yan daga cikin cikan da'a a  kiyaye ta daga dukkan abin da zai tawaye ta ko ya warware ta  mai azumi yana da tsananin bukatan  kiyaye ibadar sa da kiyaye azumin shi daga abubuwan da za su kyata shi  ko bata shi  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  ya ce:- (Idan ranar da dayan ku ke azumi ne kada ya yi batsa  kada kuma ya yi hayaniya  , idan wani ya zage shi ko ya nemi   fada da shi   to ya ce lallai ni mutum ne mai azumi) Buhari da Muslim ne suka rawaito .
Ya kasance daga cikin koyarwan magabata Allah ya musu rahama  idan sun yi azumi sai su zauna a masallatai sai su ce :- za mu kiyaye azumin mu ba za mu ci naman wani ba Imamu Ahmad Allah ya mi shi rahama ya ce :- ( Ya dace ga mai azumi ya kula da azumin shi  daga harshen shi kar ya yi musu ).
BAYAN HAKA YA KU  MUSULMAI:
Biyayya baya  cika  kuma baya tsayuwa a kan kafan sa  ya zauna da gindin sa face da kauna  wanda za ta yi riko da ma'abocinta zuwa ga ikhlasi ,  da kuma gaskiyan da zai yi nuni da kyakkyawan  bi, kuma  aiki baya kasancewa kusanci sai idan har abin da ya sa a ka yi shi imani ne ba al'ada ba ko son rai  ba kuma neman suna ba ko  don  riya ba ,  har sai ya kasance babban manufan yin shi shi ne neman lada a wurin Allah  da kuma neman yardan sa ,  idan imani da neman lada ya hadu a aiki  , sai karbuwan aikin da kuma gafara ya tabbata.
Ina neman tsarin Allah daga shaidan abin jefewa
(Ku yi gaggawa zuwa ga neman gafara daga Ubangijin ku  da aljanna wanda fadin ta   sammai da kasa an tanade shi ga masu takawa).
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo sun tabbata ga Allah bisa kyautatawan sa  godiya kuma ta tabbata a gare shi bisa datarwan sa  da baiwan sa , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya  ina mai girmama sha'anin sa , na shaida Annabin mu Muhammad bawan sa ne kuma Manzon sa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi  da iyalan sa da sahabban sa da aminci tabbatacce mai kari .
YA KU MUSULMAI
Duniya za ta kare da farin cikinta da  bakin cikin ta  shekaru kuma su kare da tsawon su da kuma gajartan su , kowa ya hadu da Ubangijin shi  to anan ne fa dukiya ba zai yi amfani ba ko da  sai wanda ya zo wa Allah da zuciya  lafiyayye , to ku fiskanci watan ku da tuba na gaskiya , ku kulla azama  bisa ribatan shi da raya lokutan shi da da'a  rayuwan duniya fa ba wani abu ba ne sai wani 'yan numfasawa ne kididdigaggu da kuma ajali iyakantacce  to ku ribaci lokuta mafi daukaka , kuma hasararre shi ne wanda ya riski watan azumi ba a gafarta mishi ba .
 Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-( Hancin shi ya dumbuli kasa, hancin shi ya dumbuli kasa , mutum da ya riski ramadan har ya fita ba a gafarta mishi ba)  Tirmizi ne ya rawaito
(Duk wanda bai bar fadin  zur ba da  aiki da shi ba , to Allah baya bukatan   ya bar abin cin sa da abin  shan sa ) buhari da muslim ne suka rawaito
Mafi girman Abin da ke gyara  zuciya ambaton Allah, da lazimtar kur'ani mai girma, da tsayuwan dare , da zama da salihai.
Sannan ku sani hakika Allah ya umarce ku da salati da aminci ga Annabin shi.