الجمعة، 25 مايو 2018

Ma'anar azumi da abubuwan lura da ya kumsa.


Hudubar Juma'a na  Masallacin Annabi na shaikh Muhammad Salah Al-Budair 9-9-1439AH
Ya ku masu azumi … farkon ramadana ya shude, har mun doshi na gomansa,
To a gaggauta a yi hanzari a yi kukan kura a dage, ku yi tsere cikin watanku kafin ya nade darensa  da tabarmarsa, ku gaggauci ramadana kafin ya tafi, ku ribace shi kafin ya shude,
Ya ku masu azumi !
Abin mamaki ga wanda zai riski ramadana azuminsa bai gyara shi ba, tsayuwansa bai girgiza shi ba, ranakunsa bai sanja  shi ba!
Abin mamaki ga mutumin da zai riski ramadana kuma yana kwadayin Aljanna da gafara da 'yantawa daga wuta amma ya sarayar da shi cikin  wasanni da da abubuwan da aka hana da haramtattu,
Ya kaiton wanda alherin ramadan ya tsere mishi!  ya hasaran wanda ya sarayar da watan ramadan!
An karbo daga Abu huraira Allah kara yarda a gare shi ya ce Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce  (Hancin shi ya  dongwali kasa; mutumin da aka ambace ni bai yi min salati ba, Hancin shi ya  dongwali kasa duk mutumin da ramadana ya shiga har ya fita ba a gafarta masa ba,hancinsa ya dangwali kasa wanda ya riski iyayensa biyu sun girma   basu shigar da shi  Aljanna ba) Tirmizi ne ya rawaito.
Ya wanda ke tambaya game da kurar hanya da tankaden gari da hadiyar nyawu ko suna bata azumi ko aa? Ya kai mai kiyaye kananan abubuwa  kuma ka yi sakaci a abubuwa masu girma! to ka kiyaye daga manyan zunubai  na alfahasha da laifuka, ka kiyaye daga cin dukiyan dan'uwanka musulmi, da cin mutuncin shi, da zambatan shi da zaluntarsa, da yaudararsa da mishi dabara.
Shin ko ya yi azumi mutumin  da ya kame daga ci ko sha a wunin ramadana alhali bai daina sakaci da yaransa ba ya barsu gurin matarsa da ya saka ba tare da kyautatawa ko tausayi ba ko tambaya game da su ko ciyarwa ba?
Shin ko ta yi azumi wacce ta haramta wa yaranta ganin mahaifinsu da ya sake ta ko ziyartarsa, ta karfafe su gun keta zarafin mahaifi da kuma fasikanci,?
Shin ya yi azumi mutumin da ya hana yaransa ganin mahaifiyarsu  da ya sake ta wacce ba dadi ga rayuwarsu sai da shinshinan  kamshinta, da ganin fiskanta da jin duminta irin na tausayi.
Shin ya yi azumi mutumin da ya kaurace wa matarsa ya kyale ta abar  zalunta an tauye hakkinta ratayayya ita ba mata ba kuma ba a sake ta ba.
Shin ya yi azumi wanda ya ci zarafin iyayen shi ya kaurace musu ya musu dagun kai, ya kuntata don yi musu hidima, in an tambaye shi yayi rowa, in an zarge shi sai ya yi wauta, in an sa rai game da shi sai ya basar, in an neme shi sai ya faku, bai amsawa sai da nuna isa, bai bayarwa sai don tsoro, bai san wani abu ba face " sai nan gaba".
Shin ya yi azumi kenan mutumin da ya yi bacci ya bar sallan farilla? Ko lokacin salla ya fita bai yi azahar da la'asar ba sai a bayan lokacinsu?  Kuma ya saba kan haka a cikin watan ramadan gaba daya.
Shin ya yi azumi mutumin da ya cinye  dukiyar gado na 'yan uwansa  maza da mata, ya yi fashin dukiyan marayu da miskinai, yayi sama da fadi da dukiyan wakafi, da hurumin masu hakki?
E, ya yi azumi da yake na sauke nauyin wajibi amma azumin da ke cakude da karya da alhaki da zalunci, wanda ke hade da manyan zunubai da laifuka masu girma.
Watakila ladan  azumin nasa ba zai kai  nauyin alhakin zaluncin sa ba da laifin sa .
 Ku ji tsoron Allah ya ku  wadan da suka rike baki daga abubuwan da suke  karya azumi da masu bata su  yayin azumi,  ku ka kuma  aikata abin da ya wajaba ga  musulmi   ya nisance shi    kuma ya haramta a gare shi ya aikata su  ko yaushe  .
 Yi salla irin sallan mai fata da tsoro*** Kafin ka yi azumi ka yi  azumi daga dukkan alfasha
 An karbo daga Jabir Allah ya kara yarda a gare shi y ce :( Idan ka yi azumi   to jinka da ganin ka da harshen ka su ma su yi azumi daga  karya da laifi  kada ka cutar da hadimin ka   ya zamana a gare ka akwai girmamawa da  natsuwa a wunin azumin kar ka sanya wunin da ka ke shan ruwa  daya da wunin da kake azumin)  .
An karbo daga hafsa  'yar Sirin ta ce : ( Azumi  garkuwa ce muddin mai ita bai ketata ba ; ketata shine yi da  wani).
  An karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :  Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Wanda bai bar fadin karya ba da aiki da ita  to Allah bai bukatar sa  da ya bar abincinsa da abin shan sa ) Buhari ne ya rawaito .
 Ya wanda ya kame daga ci ko sha  a yinin  ramadana  to ka kame daga zalunci da haramun  ka kuma kame daga fin karfin mai rauni da karbe hakkin sa ba tare da yardan sa ba .
 Ya wanda ya yi azumi daga ci *** ina ma a ce ka yi azumi daga zalunci
Ko azumi zai yi amfani ga wanda ya yi zalunci *** cikin sa na cike da laifuka
Idan har bai kasance game da ji na a kwai kurumcewa ba  a idanuwana akwai rintsawa ***  a furuci na akwai  kamewa 
 To kaso na game da azumi na kawai shi ne yunwa da kishir ruwa*** ko da na ce ni na yi azumi to ba fa azumin na yi ba .
Allah ya sanya ni da ku cikin wadan da suka yi azumin ramadana  suka kiyaye shi  ba su gurbata ayukan su ba da kyautatawan su ba  da zunubai,  ina  fadin abin da kuke ji kuma ina neman gafarar Allah , to ku nemi gafarar sa  lallai shi ya kasance  ga masu komawa gare shi mai yawan gafara ne.
 Huduba ta biyu
 Ya ku musulmai :
  Wannan lokaci ne na komawa ga Allah  wannan ruwa ne na wanka mai sanyi da kuma sha .
 Ya wanda zunubai ya daure shi, ya wadan da ayukan ababan kunya suka  kulle shi , wannan wata ne da ake kwance daurarre mai sabo,
Ya wanda ya saba  da zunubai da laifuka  , ya wanda ya wayi gari ya sammaka cikin kurakuran shi yana mai nadama   ka tuba  gaba gare ka  ga bukatar ka da kuma riba , Allah yana so ya  yi kyauta da kuma  rahama  , kuma ya yi afuwa ga masu tuba   don falala daga gare shi da kuma karamci .
 Dadi ya tabbata ga wanda ya wanke zunuban shi  a cikin ramadana  da tuba  ya dawo daga kusa kuran shi kafin kwacewan lokaci.       


الجمعة، 18 مايو 2018

FALALAR AZUMIN RAMADAN


Hudubar Masllacin Annabi 2-Ramadan -1439AH
Hudubar Farko:
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah Madaukakin sarki,  muna gode mishi kuma muna neman taimakonsa ,  kuma muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu , da munanan ayyukanmu , duk wanda Allah ya shiryar da shi babu mai batar da shi , duk wan da ya batar kuma babu mai shiryar da shi , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya , kuma na shaida Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da sahabbansa  da aminci tabbatacce mai yawa,
Bayan haka ku ji tsoron Allah - ya ku bayin Allah - hakkin tsoronsa, ku yi riko da igiya mai karfi na musulunci.
Ya ku musulmai!
Ranaku da dararraki na tafiya cikin sauri, shekara na nade watanninsa daya bayan daya, a cikin haka Masu bauta  kuma suna komawa ne ga Allah, ba da jimawa ba zasu je su riski ayyukansu,
Na daga falalar Allah da karamcinsa ya  zaba musu zamuna da lokuta na da'a, ya zabi wasu ranaku da dararraki da wasu sa'o'I don kara kaimin kwadayin ibada da kimtsawa, masu munafasa kuma suna tsere gurin ayyukan alheri , a duk lokacin da jinjirin watan ramadan ya bullo sai ya buso mana wasu kyauta masu albarka, sai musulmai su fiskance shi zuciyarsu na cike da farinciki da annashawa,  zai iya yiwuwa wani sa'a na karbar aiki ya riski bawa  sai ya kai wasu darajoji na yarda da walwala.
Wata  mafi daraja da tsarkaka ta sauka gare mu,lokaci ne mai girma Allah ya kebance ta da karramawa da daukakawa,sai ya turo manzonsa a cikinta ya saukar da littafinsa, ya farlanta azumtanta,  sa'o'inta na da albarka, duk lokutanta ana raya su da alheri ne, alheru na bibiyan juna a cikinta, albarka na gamewa a cikinta, wata ne na ihsani da sadaka zamani ne na neman gafara da kankaran zunubai,  wuninta azumi ne darenta tsayuwa ake yi, ana raya ta da Alkur'ani, ana bude kofofin Aljanna a cikinta, ana rufe kofofin wuta,ana daure shaidanu da mari a cikinta, akwai dare a cikinta  da yafi wata dubu alheri, duk wanda aka hana alherin cikinta to lalle katangagge ne daga samun alheri.
Ramadana fage ne mai yalwa don tsere cikin aikin da'a, kyauta ne na gyaran zuciya daga dauda da matsaltsalu,wata ne mai karamci ana ribanya ayyuka a ciki, ana kankare kusakurai a ciki da laifuka, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:(salloli biyar da juma;a zuwa wata juma'a  da ramadan zuwa wani ramadan na kankare abin da ke tsakaninsu muddin an nesaci manyan zunubai) Muslim ne ya rawaito
A cikin watan ne musulmai ke sauke nauyin daya daga cikin rukunan musulunci, kuma wani abu ne na bayyane da ke nuna girman wannan addini, da kuma hada kan musulmai, a nan ne fadin Allah Madaukaki sarki ya ke bayyana  (Lalle wannan al'umarku ce guda daya kuma nine Ubangijinku ku bauta min)
  Ribatan lokutan alheri  budi ne daga Allah ga wanda ya so daga cikin bayinsa,a cikin ramadan na ne tushen Ibadoji  mafi girma ke gamewa  ga salihan bayi.
Salla sadarwa ne tsakanin bawa da Ubangijinsa,ba ta rabuwa da musulmi a dukkanin rayuwarsa, sallar mutum cikin jam'i  farilla ne tana daidai da sallar mutum a gidan shi da kasuwan shi sau ashirin da bakwai, ya dace da musulmi  ya nemi taimako da salla bisa azumin shi , kuma ya zama yana da kaso mafi girma na salla a darensa, To (wanda ya yi tsayuwan dare na ramadana cikin imani da neman lada an gafarta masa abin da ya gabata na daga zunuban shi) Bukhari da Muslim ne suka rawaito
(Wanda ya yi tsayuwan dare tare da limami har ya tafi to an rubuta masa tsayuwan dare)Tirmizi ne ya rawaito.
Zakka da sadaka tsarkaka ne ga dukiya da habaka, wadata ne ga zuciya da tsarkakuwa tasirinta a bayyane yake ga zuciya da dukiya  da yara, mai tunkude bala'i  mai janyo  yalwa, wanda ya yi kyauta  ga bayin Allah, Allah zai yi mishi kyauta, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :  Allah Madaukakin sarki ya ce ya kai dan Adam ! ka ciyar zan ciyar da kai.)Bukhari da Muslim suka rawaito
Dukkan mutum yana inuwar mutuwarsa ne ranar Alkiyama, to ku yi sadaka da da dan kadan ne, ka  dadawa rai da ita, ka taimaki maragalihu,  (Duk wanda ya ciyar da mai azumi yana da kwatankwacin ladan shi)
Kuma yana daga cikin koyarwarsa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi akwai  ciyarwa da kyauta, yana bayar da kyauta irin kyautan wanda bai tsoron talauci, in ya zo bada kyauta sai ya yalwata, in ya bada sai yawaita. Ba ya maida mai tambaya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ,ba a taba tambayarsa wani abu ba face ya bada,
Manzon Allah ya fi kyauda a cikin ramadana, ya kasance a cikinsa mai kyauta kamar iska mai kaiwa ga kowa.
Azumi shi ne ibada mafi girma a wannan wata  mai falala, Musulmai na guzurin takawa a cikinsa, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Ya ku wadanda suka yi imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabtawa wadanda suka gabace ku ko zaku ji tsoron Allah)
Ladansa ba iyaka ko kididdiga, Allah ya ce a hadisul kudsi : (Dukkan aikin dan adam na shi ne sai azumi  don shi nawa ne ni zan saka game da shi)Bukhari da muslim ne suka rawaito.
(Wanda ya yi azumin ramadana cikin imani da neman lada daga Allah  an gafarta masa abin da ya gabata na daga zunubansa)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Azumi na shamaki tsakanin ma'abocinsa da sharri da zunubai, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi (Azumi garkuwa ne)Tirmizi ne ya rawaito
Ba abin da ya fi  wani  ya  nemi taimako da shi bisa takawa da kiyaye dokokin Allah da nesatan abubuwan da Allah ya haramta  kamar  azumi, Ibnul kayyim Allah ya mishi rahama  ya ce : ( Amfaninsa ya fi karfin iyakancewa  yana da tasiri na ban mamaki  wurin kiyaye lafiya.)
A lahira zai yi ceto ga ma'abotansa, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Azumi da Alkur'ani suna ceto ga bawa a ranar Alkiyama sai azumi yace ya Ubangiji na hana shi abinci  da sha'awarsa a wuni to ka cece shi don ni, sai Alkur'ani ya ce : Na hana shi barci da dare to ka bani cetonsa,  yace sai a basu cetonsa.Ahmad ne ya rawaito.
Na daga cikin ayyuka na kwarai da ake ribata akwai umra , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace : (Umra a ramadan na daidai da hajji)Bukhari da Muslim ne suka rawaito
Kur'ani maganar Allah ne kuma hujjarsa  ne a kan bayinsa, shi ne mabubbuga na hikima, mu'ujiza ce na sakon manzanci, babu hanya zuwa ga Allah sai ta gun shi, babu tsira gare mu ba tare da shi ba, haske ne  na basira da kuma gani  wanda ya kusance shi zai samu  daukaka  wanda yayi riko da shi zai samu buwaya   tilawar sa lada ne da shiriya, bitar sa kuma ilimi ne da tabbatuwa  aiki da shi   kariya ne da aminci  ilmantar da  shi  da kira zuwa gare shi kambina a kawunan masu biyayya  ,   a ramadana  ana karfafa yawaita karanta shi  da tadabburi da neman iliminsa  da kuma ilmantar da shi da aiki da shi  da kuma bin koyarwar sa  a cikin shi ne ya sauka , Allah madaukakin sarki ya ce: ( watan ramadana da a ka saukar da alkur'ani a cikin ta  shiriya ne ga mutane da  bayyanannu na daga shiriya da rarraabewa).Jibrilu amincin Allah su tabbata a gare shi ya kasance yana bitan alkur'ani tare da Annabinmu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi sau daya a kowace  shekara ,   a shekarar da ya rasu a cikinta  ya yi bita tare da shi  sau biyu   tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi .
    Addu'a ibada ce kuma kusanci ce , wata ganima ce da ba tare  da  wahala ba  kuma riba ce wanda babu asara a cikin ta , yana  janyo sauki kuma makiyi ne ga dukkan wani bala'I  ba wanda zai halaka muddin yana adu'a,  da shi ne bawa yake riskan burin shi ya samu bukatar sa  , sau da yawa yakan  kusanto da abin da yake nesa  kuma sau da yawa yakan saukake abu  mai wahala sau da yawa kuma yakan yaye bakin ciki  mafi karbuwan adu'a shi ne wanda aka yi shi  a cikin karshen dare , idan bawa ya marairaice a gaban Ubangijin shi  , sai Allah ya  amsa mishi bukatar sa ,  idan rayi ta ji yunwa sai zuciya ta tausasa ta kwanta  mai azumi ba a maida adu'ar sa har zuwa lokacin buda baki  Ibn Rajab Allah ya mishi rahama  ya ce : (   Mai azumi a daren sa da yinin sa yana cikin ibada ne  , ana  amsa adu'ar sa  a azumin sa haka kuma yayin buda bakin sa  , to shi a wunin sa yana azumi kuma yana mai hakuri  a daren sa kuma  mai ciyarwa ne kuma mai godiya )
Wanda ya yi gamon-katar shi ne wanda ya kwankwasa kofar sama, ya sanya wa kansa a wadannan ranaku da dararraki wani abin adana.
Ambaton Allah ibada ce mai girma mai sauki,duk wanda ya ambaci Allah to Allah zai ambace shi, bawa idan bai shagaltar da harshensa ba da anbaton Allah ba to kuwa zai shagaltar da shi da magana mara amfani da na sabo.
Addini muamala ne, mafi  cancanta ihsaninka cikinn halittu shi ne wanda Allah ya gwama hakkinsu  da na shi, Iyaye biyu Aljannaka ne kuma wutar ka ne, su suka fi cancanta ka kyautata musu cikin mutane, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi,ya ce : (Hancinsa ya dumbuli kasa ! Hancinsa ya dumbuli kasa! Hancinsa ya dumbuli kasa! Sai aka ce da shi wane ne? wanda ya riski iyayensa biyu sun girma ko daya daga cikinsu ko su biyun   bai shiga Aljanna ba),Muslim ne ya rawaito.
(zumunci na hade ne da Al'arshi ne tana cewa ya Allah duk wanda ya sada ni ka sada misi, wanda ya yanke min ka yanke mishi)Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
(wanda zai burge shi da a yalwata mishi a arzikinsa,  a jinkirta masa a bayansa to ya sada zumuncinsa) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Na daga cikin cikan daa  a kiyaye su daga dukkan abin da zai tawaye su ko ya warware su
Mai azumi ya fi tsananin son ya kiyaye ibadarsa da azuminsa daga abin da zai keta alfarmansa ko ya bata shi, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( a ranar da dayanku yake azumi to kada  yayi batsa, kada ya yi hayaniya, idan wani ya zage shi ko ya nemi fada da shi,  to yace ni mutum ne, mai azumi ne  )  Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Na daga cikin koyarwar magabata Allah ya musu rahama idan sun yi azumi sai su zauna a masllaci sai su ce : Mu kiyaye azuminmu kar mu ci naman wani, Ahmad Allah ya mishi rahama ya ce : Ya dace ga mai azumi da ya bibiyi azuminsa ya bashi kulawa tun daga harshensa  kada ya yi musu, ya dace ga mai azumi idan ya yi azumi ya kiyaye jinsa da ganinsa   da harshen sa da dukkan  gabbansa , kada ya sanya ranar azumin sa kamar ranar shan ruwan sa , 
Bayan haka ya ku musulmai :
 To lallai biyayya bata kasancewa cikakkiya  kuma bata tsayawa akan kwabrinta  da kuma gun da ya dace sai tare da kauna wanda za ta kai ma'abocinta zuwa ga ikilasi  da gaskiya  wanda ke haifar da kekkewar bin sunna , aiki baya kasancewa na kusanci har sai tushen shi  da ma'ingizan shi ya kasance imani ne ba al'ada ba da son rai , ba kuma neman suna ko yi don riya ba   kuma har sai ya kasance manufar sa  shi ne neman lada gun Allah da kuma yardar sa  idan imani ya hadu da neman lada a aiki to nan ne karbuwa yake tabbatuwa da kuma gafara .
         INA NEMAN TSARIN ALLAH DAGA SHAIDAN ABIN JEFEWA
(Ku yi gaggawa zuwa ga gafara daga Ubangijin ku da aljanna  da  fadinta  sammai da kassai  antanajeta ga masu tsoron Allah ).
Allah ya sa mini albarka ni da ku a cikin al'kur'ani mai girma


HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata  ga Allah bisa ga kyautatawan sa  godiya ta tabbata a gare shi bisa ga datarwansa   da kuma baiwarsa  na shaida babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake bashi da abokin tarayya  ina mai girmama sha'anin sa  , kuma na shaida Annabinmu Muhahammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne  tsira da amincin Allah su tabbata  a gare shi  da iyalan shi da sahabban shi da aminci tabbatacce mai kari .
  YA KU MUSULMAI :
Duniya za ta kare da jin dadin ta da kuma bakin cikin ta shekaru za su kare da   tsawon su da gajertan su  kowa ya je ya hadu da Ubangijin su to a wannan lokacin ne fa dukiya ba zai yi amfani ba ko 'ya'ya face wanda ya zo wa Allah da zuciya  lafiyayyiya  , to ku fiskanci watan ku da tuba na gaskiya  , kuma ku kulla azama bisa ga ribatanta da kuma raya lokutan ta da biyayya , rayuwan duniya ba wani abu ba ne face wasu numfashi  kididdigaggu da kuma ajali  iyakantacce  , ku ribaci lokuta masu daraja   ku sani  kuma ku yi fata kuma ku yi bushara  , hasararru su ne wadanda suka riski ramadana ba a gafarta musu ba , Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :  (Hancin shi ya  dongwali kasa duk mutumin da ramadana ya shiga har ya fita kafin a gafarta masa ) Tirmizi ne ya rawaito
 (Duk wanda bai bar fadin karya ba da kuma aiki da shi to ba ruwan Allah da ya bar abin cin sha da ruwan shan sa ) Bukhari da Muslim suka rawaito .
Mafi girman abin da zai gyara zuciya shi ne ambaton Allah da kuma lizimtar alkur'ani mai girma, da tsayuwan dare,  da zama da mutanen kwari .
Sannan ku sani ; lallai Allah ya umarce ku da salati da aminci ga Annabin sa ………
  

الجمعة، 4 مايو 2018

SURATUL MA'UN (AKIDA DA HALAYYA)


Hudubar Juma'a  a Masallacin Annabi tare da shaikh Abdulbari dan Awad Assubaiti 18-8-1439 AH
Allah ya saukar da littafinsa mai girma don shiryar da Dan-Adam , surorinsa haske ne, ayoyinsa fayyacewa ne, kuma ruwan marmaro  ne da bai  fakewa, mashayan ruwa ne da bai bushewa, ko gurbacewa, wanda ke cikin damuwa da bakin ciki in ya fiskance shi zai samu warakarsa cikinsa, haka wanda ke cikin bacin rai in ya koma masa zai samu  abin da zai rarrashe shi a cikinsa ya bashi annashawa.
Na daga cikin gwalagwalai masu tsada da ban kaye da ke cikin Alkur'ani akwai suratul ma'uni,
( Bamu labarin wanda yake karyatawa da ranar sakamako.
Shi ne wanda yake ingije maraya.
Ba ya kwadaitarwa bisa ga ciyar da miskini.
To azaba ta tabbata ga masallatan nan.
Wadan da suke rabkana ga barin sallarsu.
Wadan da suke riya kuma suke hana agaji.) Alma'un 1-6
Sura ce mai girma tsarin gininta ta bayyana auratayya mai karfi da ke tsakani kuduri da halayya,
Wanda ke karyata ranar sakayya shi ne mai karyata ladan Allah da ukubarsa, kuma ya karyata hisabi, imani da ranar lahira bai zauna da gindin shi ba a cikin zuciyarsa, mummunar kuduri na kai ga lalacewan aiki, lalacewan aiki alama ne na lalacewan kuduri.
Me yasa aka sifanta shi da mai karyata sakayya, sabo da yana karyata addini ne, sabo da a rayuwansa bai yi wani abu da ke hukunta yana yin addini ba kamar ya tabbatar da haka da harshensa kuma zuciyarsa ta gaskata,sai dai bai aiwatar da jikinsa ba abin da addini ya kumsa  na halayya da dabi'un addini ba, da bada hakki na imani da ke kansa ba, da bin tafarkin alkur'ani, kuma kowa ya sani imani fadi ne da harshe da gaskata wa da zuciya da aiki da gabbai.
Wanda imaninsa da hisabi da sakayya  ya yi rauni  to shi ne mai karyata addini, wanda zuciyarsa ta kekashe ta dunkule ta bushe, na daga cikin sifarsa yana ingije maraya ya walakanta shi ya cutar da shi, shi bai iya da imaninsa mai rauni da ya kyautata  rayuwarsa da halinsa, ya tsoraci mummunar aiki,
To ina kimar addini idan tasirinsa bai bayyana ba a halaye da dabi'u ba?
To ina hakikanin imani idan bai sa mutum ya yi laakari da waninsa ba har ya yi mishi alheri ba da aikata ihsani da ciyar da miskini kai da kwadaitarwa bisa ciyar da miskini, ko da a ce abin da Allah ya nema a yi abu ne na abin duniya to yin shi alama ne imani.
Imani da tadawa da sakayya shi ne  zai ja ka zuwa ga gaskiya, wanda zai dasa fiskantar ayyukan kwarai har ya zama mishi jiki, idan ya taso a kai, ba zai mishi wahala ba zai tsarkaka  ba tare da wani nauyi ba.
Kekashewar zuciya na kaiwa zuwa ga gafala da karyata addini, maganin haka na cikin hadisin mafificin halitta,Manzon halitta  Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, lokacin da wani mutum ya koka mishi bushewar zuciyarsa sai ya ce: Ka shafa kan maraya ka ciyar da miskini) Albani ya rawaito cikin sahih Attargib wattarhib.
A fadin Allah : (ba su kwadaitarwa bisa ga ciyar da miskini) akwai nuni ga cewa musulmi ana so ya kwadaitar da waninsa wurin yin ihsani, hakan kuma ba zai sauke nauyin da ke kansa ba aikata alheri ga masu rauni na daga marayu da miskinai gajiyayyu tare da kiyaye mutuncinsu da  yin nesa daga karya zukatansu, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Magana kyakkyawa da gafara ya fi alheri kan sadaka da gori ke binta)
Mafi suran ihsani shi ne taimaka  musu da kayan masrufi da zai taimaka musu don tafiyar da rayuwarsu, da samar musu da hanyoyi na  aiki ga zauna gari banza daga cikinsu da tattala su da shirya su da samar musu da kayan aiki.
(To azaba ta tabbata ga masallatan nan). Na daga cikin sifofinsu suna yin salla ne na jeka na yika,ba tare da aikata abin da sallar ta kumsa ba,ta wofinta daga hakikanin manufarta.rukunanta kuma a tawaye. Wani mutum ya shiga masallaci ya yi sallah a halin Annabi na zaune a gefe, sai ya zo yayi mar sallama sai Annabi ya ce: ( Je ka sake sallah don ba salla ka yi ba.) Bukhari ne ya rawaito.
Wanda ya yi lura da halin wadanda basu taimakawa marayu kuma basu ciyar da miskini, suna zamba kuma suna karya, kuma suna saba alkawari, kuma suna zalunci zai samu suna rabkana ga barin sallarsu.
Duk wanda ya tawaye sallarsa to sai ya fi tawaye  duk wani abu  komabayanta.
Idan ibada ta rasa ma'anarta  sai ta zama kawai motsa jiki ne da ba karfafan imani ko gyaran hali, sai tasirinta ya raunana a rayuwa, nassoshin kur'ani da hadisi sun bayyana hikimar shar'anta ibadoji  da kuma manufofinta da tasirinta a rayuwar mutane, kuma wasu makarantu ne na tarbiyya, Allah Madaukakin sarki ya ce : (ka tsaida sallah don sallah na hana alfahasha da munkari)
Allah ya ce game da azumi (ya ku wadanda suka yi imani an wajabta muku azumi kamar yadda aka wajabtawa wadanda suka gaba ce ku ko zaku ji tsoron Allah)
Manzon Allah tsira da amincin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : (Duk wanda bai bar fadin karya ba da aiki da ita to  Allah bai da bukatar ya bar abincinsa da abin shansa) Bukhari ne ya rawaito.
Allah ya ce : Karbi sadaka daga dukiyoyinsu ka tsarkake su da ita ka kwalle su daga tsatsar zunubai).
Yace game da Hajji : (Namanta ba ya tarar da Ubangiji ko jininta sai dai tsarkakar niyya ce take samunsa daga gare ku) Hajj  37
Sallah ita ce karshen abin da zaa  rasa na daga addini, idan  ta tawaya to addini gaba daya ya tawaya, Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :(za a kwance igiyar riko na musulunci gaba gaba, a duk lokacin da wata igiya ta kwance sai mutane su riki wacce ke bi mata, wacce zata fara warwarewa ita ce hukunci na karshe ko ita ce sallah)     
  Ingantacce ne Albani ya rawaito shi cikin Attargib Wattarhib kuma yana da wani hadisi da zai karfafe shi a matsayin shahid.
Idan an datar da bawa  gurin yaki da musibar  rabkanuwa daga barin ibada to suratul Ma'un zata tunatar da shi game da gyaran zuciyarsa daga riya  da fadin Allah (Wadan da suke riya) wato masu yin riya a cikin sallah da waninta :ta hanyar aikata abu da yin shi ba don Allah ba,sai don neman yardar mutane, Riya na daga cikin manyan zunubai na zuciya, yana rusa aiki ya hana shi samun karbuwa a gurin Allah. Na daga cikin abin da ayar ke nuni gare shi muna fahimtar niyyar da ta cakuda da riya na sauya aiki nagari ya koma sabo, wanda ma'abocinta ya cancanci bone. Allah Madaukakin sarki ya ce :   
(To azaba ta tabbata ga masallatan nan.
Wadan da suke rabkana ga barin sallarsu.
Wadan da suke riya).
Haka nan ne zuciyar da ta rasa ikhlasi maganar ta ba ta da kimai, ibada ba zata yi wani tasiri ba a halayenta, kuma ba zaa karbi aikinta ba, ba tsarkaka ga ruhinta.
Na daga cikin mabudi mafi girma na nasara : a datar da bawa ga jan ragamar sha'awarsa ta riya ya ja mata linzami, kuma ya mika wuyarsa ga Allah, ya yi ikhlasi a aikinsa, niyyarsa kuma ya fiskance shi da ita, ya tace ta daga neman wata ganima, ko sha'awa ko matsayi ko dukiya, ko suna, ko samun matsayi cikin zukatar mutane, ko neman yabonsu, ko gudun zargi a gare su, Allah Madaukakin sarki na cewa a hadisin Alkudusi: (ni ne mafi wadatuwa daga abokan tarayya, duk wanda ya yi wani aiki ya hada ni da wani a ciki to na bar shi abokin tarayyar tasa) Muslim ne ya rawaito.
Huduba ta biyu
Karshen aya ta wannan sura na nuni ga muhimmanci halye na gari ga al'uma, ta hana zamewa kankamo, Allah Madaukakin sarki ya ce : ( kuma suke hana agaji.) wato suna hana bada aron abin da mutane suke arawa junansu, cikin abin da ba a saba hana wa ba a al'adance.
Wadannan  basu kyautata bautan Ubangijinsu ba, basu kuma kyautatawa halittunsa ba, ta hanyan bada aron abin da zaa amfana da shi  a taimaka da shi, tare da wanzuwar  abin a komo da shi ga mai shi,  to wadanna n mutanen  sun fi kusa da hana bada zakka da abubuwa na neman kusanci sama da wani abu,   
( Bamu labarin wanda yake karyatawa da ranar sakamako.
Shi ne wanda yake ingije maraya.
Ba ya kwadaitarwa bisa ga ciyar da miskini.
To azaba ta tabbata ga masallatan nan.
Wadan da suke rabkana ga barin sallarsu.
Wadan da suke riya kuma suke hana agaji.) Alma'un 1-6
   
  

الجمعة، 20 أبريل 2018

sha'aban wata ne na kimtsawa don ramadan


Hudubar juma'a  na Masallacin Annabi tare da sheikh Abdullah Bin Abdurrahman Albu'aijan 4-8-1439AH
Hudubar farko
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, wanda ya sanya jinjirin – wata  lokuta ne ga mutane da kuma sanin kidayan  zamani, shekaru da watanni , ya sanya dare da wuni  mayau ga wanda ya ke  nufin ya wa'azantu ko ya ke nufin  godiyar    ni'imar  Ubangiji  , na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin tarayya , ya sanya rana ya zama mai tsananin haske da wata kuma mai haske   na shaida Annabi Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne  , ya turo shi da shiriya da addini na gaskiya , yana mai albishir da gargadi kuma mai kira  zuwa ga Allah da izinin shi da fitila mai haskakawa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalan shi da sahabban shi da aminci tabbatacce mai yawa .
            Bayan haka :
 Lallai zance mafi gaskiya shi ne littafin Allah , mafi kyan koyarwa shi ne koyarwar Annabi  mafi sharrin al'amura shi ne fararrun ta , kuma dukkan fararrun abu bidi'a ne  kuma dukkan bidi'a bata ne  kuma dukkan bata na wuta .
        Bayin Allah :
Ina muku wasiyya da ni kai na da tsoron Allah  mabuwayi da daukaka, domin ita ce wasiyyar mutanen farko  da na karshe  ( Hakika mun yi wasiyya ga wadan da aka bawa littafi  kafin ku da ma ku kanku da ku ji tsoron Allah ).
YA JAMA'AR MUSULMI:
Lallai  Allah na da  wasu yanki na  rahama  to ,  ku yi kokari ku same su  da wasu zamuna na alheri  to ku yi kokari ku same su  da kuma lokuta masu falala ku yi kwadayin riskan su, ga su sun  fiskanto  ku,  to ku fiskance su  ga su sun sauka gare ku to ku ribace su  domin su dinnan wasu lokuta ne kadan  da za su zo su wuce kamar kyabtawan ido,  kaito ga sarayar da rayuwa ga mutumin da  ya sarayar da ita, madalla  kuma da  wanda ya ribace ta  ya yi nasara da ita (Shi ne wanda ya sanya dare da rana mayau ga wanda  yake nufin  ya wa'azantu ko yake nufin godiyar ni'imar Ubangiji ).
                     Rajabu ya shude  to me  ka kaddamar a cikin shi  *** Ga kuma watan   sha'abanu mai albrka   
Ya kaiton wanda ya sarayar da lokuta bisa jahilci *** da alfarmar ta  ka farka  ka kuma kiyaye  albarkoki 
To da sannu  za ka rabu da jin dadi  cikin karfi *** mutuwa kuma  zai sanya ka a kana ki   ka bar gidan ka
Ka yi kokari  ka tuba daga kusakurai ***tuba irin na mai iklasi kuma ka sanya  abun riska
Bisa neman kubuta daga wutar jahima *** mafi alkairi ga ma'abota laifuka shi ne wanda ya yi kokari ya gyara.
YA KU BAYIN ALLAH
Hakika watan sha'abana ya sauka a gare ku, kuma yana cikin lokuta na da'a  da kuma lokuta masu falala,  ana neman alheri a cikin shi  ana daga ayyuka a cikin shi  da ayuka na kusanci , an karbo da Usama Dan Zaid Allah ya kara yarda a gare su da baban shi  ya ce : '' na ce ya  Manzon Allah  ban gan ka kana azumtar wani  wata daga cikin watanni ba kamar yanda  kake azumtar sha'aban''. Sai Manzon Allah ya ce  (Wannan wata ne da mutane ke gafala daga gare shi,  wanda ke tsakanin rajab da ramadana  shi ne watan da ake daga ayyuka a cikin shi  zuwa ga Ubangijin talikai , ina so  kuma a daga ayyuka na  ina mai azumi , an karbo daga Aisha Allah ya kara yarda a gare ta  ce : Manzon Allah ya kasance yana azumi har mu ce ba zai sha ruwa ba , kuma yana shan ruwa har mu ce ba zai yi azumi ba  ban ga Annabi ya cika azumin wani wata ba  sai ramadana  ban ganshi kuma yana yawaita azumi ba kamar yanda yake yawaitawa a sha'aban .
YA KU BAYIN ALLAH
Lalle watan sha'aban fage ne na kimtsawa da shiryawa don fiskantar ramadan, to shi rai na bukatar maimaci da a bi da shi mataki bayan mataki, da shimfida har ya saba da shi, haurawa zuwa sama na bukatar matakala da tsani, rayi kan kwace, jiki kan gaji  kuma mutum ya kosa daga ibada   sabo da ba abi da shi mataki -mataki ba sai ya rasa jin dadin ta  kuma ya rinka haduwa da tsananin ta , ta iya yiwuwa ma ya yanke daga  gare ta  ya kasa cigaba da ita  sai alheri mai yawa ya tsere mishi .
               Ya yin da sha'aban ya kasance  mukaddima  ne ga  ramadan  to ya dace ga musulmi ya dage a cikin ta  irin kokarin da zai yi a ramadan , matsayin azumin sha'abana ga ramadan kamar matsayin sunnonin farilla ne  ga  sallan farilla , azumtar shi na daga cikin shiri ne da kwadayi bisa ga  ramadana daya daga cikin rukunnan musulunci   kuma azumi  na  daga cikin ibadoji  da ake  neman kusanci da shi  da kuma  da'a  da ibada mafi girma,  an karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : '' Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce: ''Allah madaukakin sarki ya ce : ( Dukkan aikin dan adam na shi ne sai azumi  lallai shi nawa ne kuma ni zan sakanya game da shi ).
          (Kuma azumi garkuwa ne  idan dayan ku na azumi  kada ya yi fasikanci   kada ya yi batsa  kada ya yi hayaniya   in wani ya zage shi  ko ya yi fada da shi ya ce ni mutum ne mai azumi .( Na  rantse da wanda ran muhammadu ke hanunsa   warin bakin mai azumi ya fi kamshi a wurin Allah a kan turaren almiski),  ( mai azumi na da farin ciki biyu ; farin ciki yayin shan ruwarsa da kuma  farin ciki yayin  haduwa da Ubangijinsa) .
   YA JAMA'AR  MUSULMI:
Kofofin alheri a bude suke, kuma Allah baya sarayar da ladan wanda ya kyautata aiki  ,ga aiyuka na da'a da suke saki waiwai  ba a kayyade su da zamani ko wuri ba,  nau'ukan ayyukan da'a   suna da yawa  kuma suna fin junan su  gwargwadon lokaci  sai dai  ba wasu ibadoji na da'a da aka kebance  su da watan  sha'aban  sai dai wata ne da ake daukaka ayukan shekara a cikin ta  kamar yanda ake daukaka ayukan mako     a litinin da alhamis  ya dace mutum ya yi kwadayin  ya cika ta , sabo da haka ne Manzon Allah yake  son  azumtar shi , kamar yanda ya ke son azumtar litinin da alhamis .
    Ya jama'ar Musulmi :
Lallai gafala wata cuta ce mai wuyan magani  kuma  abu ne na laifi wanda yake mai zunubi  yana  yanke sila tsakanin bawa da Ubangijin shi ba zai rinka jin wani laifin shi  ba   ko ya yanke daga  alhakin shi ba ,  ba zai tuba daga zunubin shi  ba  ba zai yi wani ma'arufi ba ko ya yi hani ga wani munkari ba   lokutan alheri na ta wuce shi da lokutan falala  alhali yana cikin bacci na gafala  baya farkawa  yana gani baya lura ana mishi wa'azi baya wa'azantuwa ana fadakar da shi baya fadakuwa  hakika Manzon Allah ya kwadaitar game da  azumin sha'aban sabo da gafalan da yawa daga cikin mutane game da shi  sai ya ce  : (  Wancan wani wata ne da mutane suke gafala game da shi  yana tsakanin rajab da ramadana ).
         Ya mai yiwa kan shi nasiha ka gajarta buri  kuma ka farka daga gafalan ka  ka yi shiri don hisabi  kafin zuwan ajali .
      Ina neman tsarin Allah daga shaidan  abin jefewa 
(Ka tsare kanka tare da wadan da suke bautawa Ubangijin su  safiya da maraice suna nufin  fuskan Allah da ibada  ta su  kada ka juyar da idanunka da barin abokantaka ta su , kana nufin kawar duniya   kada ka bi wadan da muka rafkanar da zuciyar sa da barin ambatonmu  ya bi son zuciyar sa  a cikin shirka  al'amarin sa ya kasance faifayi )
Allah ya sa mini albarka ni da ku  a cikin alku'ani
HUDUBA TA BIYU
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah , yabon da ya dace da daukakar sa  tsira da amincin Allah su tabbata  bisa ga  zababbe cikin Manzannin sa da Annabawan sa  da iyalan sa da sahabban sa  da mabiyan sa da masoyan sa   .
YA KU BAYIN ALLAH :
 Lallai Allah  bai halicci mutum ba  ya kara mishi a tsawon rayuwa face don ya yi kokari wajen yi mishi da'a kuma ya nesanci saba mishi Allah madaukakin sarki ya ce :(Ban halicci mutum da aljani ba sai don su bauta mini)  Hakika Allah ya fifita wasu sashi na lokuta ya kwaranya musu sauki  da albarkatu da alheri mai busowa, ya shar'anta wasu hukunce-hukunce da ayyuka da kuma da'a, kuma ya yi wa bayin sa izini da su nemi  alheri a cikinta, to ku nemi alheri a dukkan zamaninku,kuma ku kutsa don karbar rahamar Allah, lalle Allah Mabuwayi da daukaka,na da wani yanki na rahamarsa da ke samun wanda ya so da ita daga cikin bayinsa.
Ya Al'uma masu kadaita Allah!
Ku kiyaye akidarku   ku rike ta da  hakwaran cin tuwo   domin ita ce tushen tsiran ku,  ku yi riko da addinin ku da littafin ku da shiryarwan Annabin ku
 YA JAMA'AR MUSULMI :
 Lallai Shaidan makiyi ne a gare ku to,  ku rike shi makiyi  domin shi dinnan yana iya kokarin shi a lokutan alheri da falala don ya batar da mutane daga shiriya ya yi shamaki tsakanin su da yanki na rahama da gafara ya katange su daga da'an Ubangijin su kuma ya sanya alheri mai yawa ya tsere musu  , sai ya batar da wasu sashi na daga  mutane ta hanyar shubuhohi  kamar yanda yake batar da wasu sashi na su ta hanyar   sha'awe –sha'awe  , sai ya fitini wasu mutane ta hanyar bidi'o'i da fararrun abubuwa   ya sarayar musu  da dama na lokutan alheri  ta hanyar bidi'o'i da sha'awe-sha'awe.
 TO YA JAMA'AR MUSULMAI :
(Hakika kuna da abin koyi mai kyau daga Manzon Allah   ga wanda ya kasance yana fatan Allah da ranar lahira )
(kuma duk wanda ya yi wani aiki wanda ba umarnin mu a ciki to an maida mishi )
To ku yi riko da sunna to fa dukkan fararren abu bidi'a ne dukkan bidi'a bata ne kuma   dukkan bata na wuta.
YA KU BAYIN ALLAH :
Duk wanda yake da ramuwa na ramadana a kansa to ya gaggauta azumtar shi  kafin shigowar ramadana  domin lokacin ya matse,  to, wajibi ne ga dukkan musulmi ya gaggauta biya  , ku yi tsere wurin ayukan alheri  ku gaggauta wurin da'a ku yi gaggawa zuwa ga gafara daga Ubangijin ku  da aljanna fadint ya kai kasa da sammai .
                YA KU BAYIN ALLAH
Hakika lallai Allah ya saukar a gare ku mafi daraja cikin littatafai ya kuma aiko muku da mafi daraja cikin manzanni ya cika muku addini kuma ya yarda da shi a gare ku  ya bayyana shi akan dukkan addinai , ya cika ni'ima  sai ya ce :  (A yau na cika muku addininku kuma na cika muku ni'imata a gare ku , na yarda a gare da musulunci a matsayin  addini)
 Hakika mun yarda da Allah shi ne Ubangiji da musulunci shi ne addini  kuma Muhammadu shi ne Annabi kuma Manzo ,
 muna rokon Allah da ya tabbatar da mu da tabbataccen zance  a rayuwan duniya  da kuma lahira , kuma ya  nisantar da fitina daga gare mu na bayyane da na boye ,  kuma ya azurta mu da riko da sunna  kuma ya tunkude mana gafala da tabewa kuma ya datar da mu  a sha'abana kuma ya riskar da mu da ramadana.
 ya  Allah ka daukaka musulunci ga musulmai  

       
      


الجمعة، 6 أبريل 2018

NI'IMAR ALJANNA


Hudubar juma'a na Masallacin Annabi  tare da sheikh Salah bin Muhammad Albudair 20-7-1439 AH.
Hudubar farko:
Ya ku Musulmai ! Ajali na kusantowa, Burace –burace na karewa, duk wani tsani ya yanke, lokacin tafiya da kaura ya zo, ya raba mutum da iyalai da sadawa da su,
Ba na ganin akwai abin da zai sha gaqban mutuwa ya tsallake ta, *
                                                                              Mutuwa ta katse jin dadi ga mawadaci da talaka.
Ka yi dubi ga duniya da idon mai ban kwana, *
                                                                      Domin hakika tafiyar ta kusa lokacin ban kwana ya yi.
Lallai Masoyi abin fizgewa ne daga masoyansa, *
                                                                                          Mai gadi ko mai tsaro bai hana  mutuwa.
Ta yaya zai yi farin ciki da duniya da jin dadin cikinta?*
                                                            mutumin da ana kidanya masa lafuzansa da numfashinsa.
Dukkan wata gida –wata rana-abar rushewa ce *
                                                         Komin dadewarta bisa ginshikinta.

Ya ku musulmai!
Yayin da duniya ta kasance gida ce ta fitintinu da jarabawa to mutum zai dandani wahalar neman abin rayuwa ,da gwagwarmaya da bala'i da cututtuka da nau'uka na musibu, da cin karo da abubuwa masu hanun riga, da kawatarwa irin na shaidan, da ma'abota barna.
Mai kyauta da karamci Mai jinkai,Mai girma ya yi kira ga bayinsa muminai zuwa ga Aljannarsa  gidan karamcinsa  gidan aminci da ni'ima, kubutacciya daga bakin ciki da bacin rai, wanda babu matsaltsalu da tashin hankali da bala'I,(kuma Allah na kira zuwa gidan aminci)
Idan duniya ta ma kunci gabadayanta *** ka zama baka da wani masauki sananne.
To ka yi gaggauto zuwa ga Jannatu Adnin  domin ita dinnan *** Masaukan mu ne na farko kuma cikinta akwai shemomi
sai dai fursunonin yaki ne na Magauda (Makiya) abin mamaki ya jama'a *** shin ko za mu koma gidajenmu mu samu aminci?
Gida ce da ni'imarta bai karewa , bai  halakewa,gidan da akwai dukkan alheri cikinta har da kari, an tanade ta an kusanto da ita an kawata ta domin karramawa ga masu tsoron Allah, ba su jin tsoron wani abu a ciki na bakin ciki ko hayaniya da gajiya,ba su tsoron talauci ko bashi a cikinta,ko fitarwa ko katsewa ko karewa ba. (Ba zaa fitar da su daga cikinta ba).
Duk wanda ya shiga Aljanna ba zai samu wata damuwa ba, tufafinsa ba zai ridddige ya tsufa ba,haka samartansa ba zai tsufa ba, mai yekuwa zai kira su : (lalle za ku samu  lafiya a cikinta ba za ku yi rashin lafiya ba har abada, kuma ku rayu ba za ku mutu ba har abada, kuma ku zama matasa ba za ku tsufa ba har abada, lalle kuma za ku samu ni'ima ba za ku samu wata damuwa ba har abada, sai a ce : Ya ku 'yan Aljanna ku dawwama ba mutuwa har abada, ya ku 'yan wuta ! ku dawwama ba mutuwa,  a cikin Aljanna akwai abin da ido bai taba gani ba, kunne bai taba ji ba,zuciyar dan Adam bai taba hararo shi ba,).
(Mala'iku na shiga musu ta kowace kofa, Amincin Allah ya tabbata a gare ku sabo da hakurin da ku ka yi, madalla da gida mai kyakkyawan karshe).
Allah Mai girma!! Mala'iku na shigo musu,!! Mala'iku su zo musu,Mala'iku  su gaishe su, Mala'iku na taya su murna!!
(To amincin Allah ya tabbata a gare ku, kun ji dadi, ku shige ta kuna masu dawwama.)
Abin mamaki da girman wannan kusancin da girmamawa a gidan aminci.
Lalle Allah Madaukakin sarki zai ce ga 'yan Aljanna,  :( ya ku 'yan Aljanna ! sai su ce : Mun amsa kirarka kuma mun rusuna, sai yace : ko kun gamsu? Sai su ce :  ta yaya ba za mu gamsu ba bayan ka bamu abin da baka baiwa wani ba daga cikin halittunka,sai yace : zan baku abin da ya fi haka.sai su ce Ya Ubangiji me ne ne ya fi hakan?, Sai yace : zan sanya yarda ta a gare ku bayan haka ba zan yi fushi da ku ba har abada).
(Kuma yardar Allah ya fi girma)
Ya fi girma bisa Aljannar da koramanta ya fi girma akan benayenta da tufafinta da guzurinta.
Amma ganin Allah a Aljanna shi ne abin da masu jan damara su ke jan damara akan shi, masu yin munafasa da rige –rige ke tsere a kan shi, ya hana shi ga wadanda aka musu shamaki da Ubangijinsu, kuma aka kore su daga kofarsa, Allah Madaukakin sarki ya ce :(Wasu fiskoki a wannan rana suna mani'imta ne. masu dubi zuwa  ga Ubangijinsu) Al  kiyama 21-22
An karbo daga Abu Musa Allah kara yarda a gare shi yace : Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : Gonakai guda biyu na azurfa kwanukansu da abin da ke cikin su,da gonakai biyu na zinari  kwanukansu da abin da ke cikinsu, ba wani abu da yake tsanin mutanen da su ga Ubangijinsu  mai tsarki da daukaka face  rigar girmame –girmame a fiskarsa cikin Aljannar Adni) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
An karbo daga Suhaibu daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :: Idan 'yan Aljanna sun shiga Aljanna Allah Madaukakin sarki zai ce : Ko kuna son wani abu na kara muku? Sai su ce : Allah ba ka haskaka fusakanmu ba ka shigar da mu Aljanna ba kuma ka tseratar da mu daga wuta? Yace sai ya yaye hijabin  sai su ji dadin da  ba a taba basu wani abu da ya fi soyuwa a gare su ba kamar ganin Ubangijinsu  ba Mabuwayi da Daukaka).Muslim ne ya rawaito.
Ibnul Kayyim Allah ya mishi rahama ya ce :  To wannan kenan in ka tambayi ranar kari daga Mabuwayi  Abin godiya, da ganin fiskarsa tsarkakakka daga misali ko kamanci, kamar yadda kake ganin rana lokacin azahar, da kuma wata a daren sha hudu, kamar yadda aka karbo daga mai gaskiya abin gaskatawa,ta hanyoyi  masu dumbin yawa, hakan na nan cikin sahihai da sunann da musnadai, na daga riwayar Jarir da Suhaibu da Anas da Abu Huraira da Abu Musa da Abu Sa'id , Ka saurari ranar da mai kira zai yi kira ? Ya 'yan Aljanna Ubangijinku  zai nemi ziyartarku,, to ku zo , don ziyartarshi,  sai su ce : mun ji mun bi,sai su taso zuwa ga ziyara suna gaggautowa  har lokacin da suka isa kwarinmai fadi  wanda aka sanya musu magama, suka hadu a can ba wani guda da mai kiran ya bari, Ubangiji Allah sai ya yi umarni da a kafa masa kujerar sarautarsa, sai aka kafa, su kuma aka kafa musu  minbarai na haske, da minbarai na lu'ulu'u, da minbarai na zubarjadi, da minbarai na zinari da minbarai na azurfa, mafi karancin daraja a  cikinsu ya zauna,-  duk da ba wani makaskanci cikinsu- bisa wata turbaya na almiski, kuma basu ganin nan kan kujera sun fi su samu kyauta,
Har zuwa lokacin da kowa ya natsu a mazauninsa hankali ya kwanta, sai mai kira ya yi kira,: ya 'yan Aljanna  lalle kuna da wani alkawari a gurin Allah da yake so ya cika muku! Sai su ce : Mene ne shi? Ase ba an haskaka fisakanmu ba,a ka nauyaya mizaninmu ba, aka shigar da mu Aljanna ba, aka nesatar da mu daga wuta ba? Suna cikin haka sai wani haske ya bayyana  wanda Aljanna ta haskaka da shi, sai suka daga kawunansu, sai ga Aljabbaru (kasaitacce) Girmansa ta kasaita, sunayensa sun tsarkaka, ya fuskanto su daga ta samansu,yace : (ya 'yan Aljanna amincin Allah ya tabbata a gare ku) Ba a amsa wannan gaisuwar da sama da fadin cewa : ya Allah kai ne aminci, daga gun ka aminci ya ke, albarka ta tabbata a gare ka,ya Ma'abocin girma da karamci,sai Ubangiji ya yi tajalli a gare su(Ya bayyana) Albarka da daukaka sun tabbata a gare shi, ya musu dariya yace :  Ya 'yan Aljanna ! sai ya zama farkon abin da zasu ji daga gare shi shine : Ina bayi na da suka yi min biyayya a fake bisa halin ba su ganni ba? To wannan ne ranar kari , sai su yi tarayya a kalma guda: Mun yarda to  ka yarda da mu, sai ya ce ya 'yan Aljanna in da ban yarda da ku ba da ba zan saukar da ku a Aljanna  ta ba. Sai yace : wannan ne ranar kari ku roke ni! Sai duk su yi tarayya a kan kalma guda: ka nuna mana fuskar ka mu yi dubi zuwa gare shi, sai Ubangiji  Allah Madaukakin sarki ya yaye shamaki, Daukaka ya tabbata a gare shi, sai ya yi tajalli a gare su, sai ya lullube su da haskensa, sai su manta da duk wata ni'ima da su ka taba gani, badon Allah ya hukunta ba za su kone ba da sun kone, ba wani da zai rage a wannan majlisar har sai ubangiji ya mar lacca kai tsaye, har ma ya ce ya wane ko kana tuna ranar kaza ka aikata kaza da kaza,? Yana tunatar da shi wasu sashi na ha'ince –ha'incen da ya yi a duniya, sai ya ce ya Ubangiji ba ka yafe mini ba? Sai yace ai da gafara tawa ce ka kai wannan matsayin taka da ka ke kai.
Allah Mai girma! Abin mamaki  da girman irin wannan ni'imar, abin mamaki da irin wannan karramawar, zasu ga Ubangijinsu a Aljanna,  za su ga Allah Ma'abocin girma da kyau da kamala, za su ga abin bautan da sun dade suna bauta masa, suna mishi tasbihi,da halala da kabbarori, suka yi mishi  sujada kuma suka girmama shi.
Wani irin dadi ne da jin dadi, wace irin ni'ima ce, wani irin rayuwa ce wani irin walwala ce,wani irin zabi ne, zasu ga Allah wanda duniya  bata yi dadi ba sai da ambatonsa,lahira ma bata yi dadi ba sai da yafiyarsa, haka ma Aljanna ma bata yi dadi ba sai da kallo zuwa gare shi, wayyo kwadayinmu zuwa gare shi, wayyo shaukinmu zuwa ga gidan ni'ima, wacce a cikinta masu kadaita Ubangiji zasu , zai yi tajalli a gare su ya bayyana, kuma yayi dariya agare su,ya fiskanta zuwa gare su, kuma yana bayyana ga 'yan Aljanna a kowace juma'a, cikin wata turbaya na Alkafur sai su kasance kusa da shi gwargwadon gaggawar su zuwa Juma'a a duniya,ba su kara dubi zuwa ga Ubangijinsu sai hakan ya kara musu karama.
Zaka ga fiskar Ubangiji  madalla da fiska da ke cike da kauna da daukaka.
Ya ku bayin Allah!
Wannan dadin labari ina ga dadin ganin?
Ya Allah muna rokon ka dadin dubi zuwa fiskar ka, da kwadayin haduwa da kai, ba cikin wata cuta ko cutarwa ba, ko wata fitina mai cutarwa ba.
Huduba ta biyu
Ya ku musulmai !
Ku kimtsa kayanku ku gaggauta morar rayuwarku  ku ribaci lokacin ku, to me ke baya ni'ima da jin dadi da kawar rayuwa da walwalarta face mutuwa da kare wa da rididdigewa,
Mutuwa kofa ce kuma dukkan mutane zasu shige ta
Me zan ji bayan wannan kofar me ke cikin gidan?
Gidan Aljanna ne na dawwama  muddin ka yi aiki da abin da zai yardar da Allah
In ka gaarta sai wuta, sune gidaje biyu mutane basu da wasu gidan in ba su ba.
To ka duba wa kanka wanne zaka zaba.