Hudubar Masallacin Annabi na shaikh Abdullah Bin Abdurrahman Albuaijan
19 safar 1441Ah.
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah
wanda ya shiryar da mu ga imani. Ya bayyana mana manyan ginshikai na gaskiya da
hujja, ya turo manzanni ya saukar da littafi a gare su tare da mizani.
Na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah,
shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, shaidawa ta gaskiya da imani, Na
shaida Muhammad bawanSa ne kuma ManzonSa ne, an turo shi zuwa ga mutane da
aljanu.sai Allah ya tseratar da mu daga dulmuya cikin bata.ya kuma kubutar da
mu daga gangarawa cikin kafurci da hasara.tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi da iyalan shi da sahabbanSa da wanda ya bi su da kyautatawa.
Bayan haka :
Lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, mafi
alherin shiriya ita ce shiriyar Muhammad dan Abdullah, kuma mafi sharrin
al'amura shine fararrunta, kuma dukkan fararrun al'amura bid'a ce kuma dukkan
bid'ah bata ce, kuma dukkan bata na wuta.
Ya ku bayin Allah! Ina muku wasiyya da ni kai
na da tsoron Allah,Mabuwayi da daukaka,domin shine wasiyyar Allah ga mutanen
farko da na karshe (Hakika mun yi wasiyya ga
wadanda aka bawa littafi gabaninku da ku kanku da ku ji tsoron Allah).
Ya jamaar musulmi!
Allah ya bawa mutum hanyoyi masu yawa na samun
ilimi.ya bashi hankali da fahimta, ya mishi umarni da neman ilimi sai ya ce : (ka yi karatu da sunan Ubangijinka mafi karamci. Wanda
ya koyar da alkalami. Ya sanar da mutum abin da bai sani ba).
Allah ya zabi mutum don ya khalifantar da shi a
doron kasa kuma ya bashi ilimi don aiki da samun daukaka, ya bashi hankali don
a fiskantar da magana gare shi a kuma dora mishi nauyi na sharia sai yace : (A yayin da Ubangijinka
yace ga Malaiku lalle Ni zan sanya mamayi a doron kasa, sai suka ce :zaka sanya
a cikinta wanda zai yi barna kuma ya zubar da jini alhali mu muna tasbihi da
godiya a gare ka kuma muna tsarkake ka,sai yace lalle ni na san abin da baku
sani ba).
Sai Allah Madaukakin sarki ya bayyana cewa samun daukaka da daraja na ga
ilimi sai yace :( Allah na daukaka darajan
wadanda suka yi imani daga cikin ku da wadanda aka bawa ilimi darajoji).
Ya ku bayin Allah!
Lalle mutum ana haifansa jahili ne bai san
komai ba, Allah Madaukakin sarki yace : ( Allah ya fitar da ku daga cikunan uwayenku baku san
komai ba).
Hakika Allah ya dauke shamaki na kadan daga
cikin ilmomi sai ya bada dama ga bayi da zasu iya riskan su, amma mafi yawan
ilimi ya boyu daga riskar mutum. Allah ya ce :
( Kuma ba a baku wani abu na ilimi ba
face dan kadan) Allah ya
kebanta da ilimin gaibi ya boye shi, ya sanya ba wanda ya san hakikanin tawilin
shi sai shi kadai. ( A gare shi mabudan gaibi
suke, ba wanda ya san su sai shi).
An karbo daga Abdullahi dan Umar
Allah ya kara yarda a gare su ya ce daga Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi yace : (Mabudan gaibi guda biyar ne. ba wanda ya san su sai
Allah, Ba wanda ya san abin da mahaifa zata rage sai Allah, ba wanda ya san
gobe sai Allah,ba wanda ya san yaushe ruwa zai zo sai Allah,ba wanda ya san rai
a wace kasa zai mutu sai Allah, ba wanda ya san yaushe Alkiyama zata tashi sai
Allah, sai ya karanta fadin Allah ( A gare shi mabudan gaibi suke,
ba wanda ya san su sai shi ya san abin da ke cikin tudu da kogi, ba wani ganye
da zai fado face ya san da shi, ko kwaya cikin duhun kasa ko danye ko busasshe
face yana cikin littafi bayyananne).Bukhari ne ya rawaito.
Na daga cikin hikima da sunnar Allah ya sanya
shamaki tsakanin gaibi da halittunSa har ma da mafi soyuwan mutum cikin
bayinSa, Ba wani mala'ika na kusa ko Annabi Manzo, (
Kace ba wanda ya san gaibi cikin sammai da kasa face Allah) kuma ya
umarci Manzon Allah da ya maida al'amura zuwa ga Allah, kuma ya bada labari
game da kansa cewa bai san gaibi ba, kuma ko tsinkayar wani abu na hakan, face
abin da Allah ya sanar da shi, sai yace : ( Kace ban mallakawa kai na wani abu na
amfani ba ko cuta face abin da Allah ya so, da ace na san gaibi da na nemi
yawaitawa daga alheri kuma wani abu mummuna bai shafe ni ba.).
Ya jamaar musulmi!
Zukata na neman sanin gaibi, kuma dukkan
boyayyen abu ana kwadayin shi, a cikin su akwai wanda shaidanu kan kaskantar da
su da mataimakansu makaryata, da bokanci da duba da masu duba da taurari da
sihiri suna kage da karerayi suna fadin abin da ba su sani ba game da Allah, ( Kace Ubangiji
na ya haramta alfahasha ne kawai wanda ya bayyana ko ya boyu daga cikin su da
laifi da zalunci ba tare da gaskiya ba kokuma ayi shirka a hada Allah da wani
cikin abin da bai saukar ba da shi na hujja ko ku fadi abin da baku sani ba
game da Allah .) kuma hakika shaidanu sun kasance suna haurawa zuwa sama sai su saci ji don su
labartawa mataimakansu na daga bokaye su kuma sai su gayawa mutane labarin to
ku saurara lallai shaidanu an hana su satan
ji kuma an yi shamaki tsakaninsu da shi tun lokacin da aka turo Annabi Muhammad
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
hakika alkura'ni ya bada labarin hakan game da su sai ya ce :( lallai mun nemi satar ji daga sama sai muka sami an cika ta da matsara masu karfi da taurari masu konewa. Hakika
mun kasance gabanta don sauraru, duk wanda yake neman saurara to wanda ya yi
sauraru a yanzu ya saci ji to zai sami
tauraru mai dako gare shi da aka dakatar da shi don a jefe shi da shi (lalle mu bamu sani ba sharri ake nufa da
wanda ke doron kasa ko kuma Ubangijinsu ya na nufinsu da shiriya ne) Allah Madaukakin sarki ya ce
: shaidanu ba su sauka da wannan
alkura'n ba kuma ba zai kamata gare su su saukar da shi
ba, kuma baza su samu ikon saukar da shi ba hakika su ababan nesantarwa ne game
da barin jin zancen mala'iku )
Hakika Allah ya hana su
zuwa sauraro zuwa ga duniyan sama ya sanya taurari abin jifa ga su ta kowani
jiha da suka fiskanci sama Allah Madaukakin
sarki ya ce (Hakika mun kawata saman duniya da adon taurari , Mun kiyaye ta daga
kowani shaidani mai taurin kai , ba za su yi sauraro zuwa ga mala'ikun sama ba
ana jefesu daga kowace nahiya, ababan korewa suna da azaba madawwamiya a lahira
, sai wanda ya fauta guda daya daga mala'iku kuma tauraru mai tsananin haske ya
bi shi)
ya ku bayin Allah imani da alkura'ni mai girma
ba ya haduwa a zuciya da gaskata wadan nan bokaye (dujjalai) sabo da haka ne Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (Duk wanda ya zo ga
boka ko dan duba ya gaskata shi cikin abin da ya ke fadi to hakika ya kafurta
da abin da aka saukar wa Muhammadu,)
Ku yi katanga da akidar ku kuma ku
yi riko da alkura'ninku kuma ku sani lallai Allah shi ne masanin gaibi ba ya
bayyana saninSa ga wani .
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya sun tabbata ga
Allah Ubangijin talikai kyakkyawan
karshe na ga masu tsoron Allah babu gaba
sai ga azzalumai, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabinmu Muhammad da
iyalansa da sahabbansa baki daya ya ku bayin Allah
Hakika an yi jarabawa ga mutane ta
hanyar shigowan bokaye da matsafa da masu duba da 'yan tsubbu sai suka yi
galaba akan masu rauninsu suna musu dako da wasa da hankulansu dukkan isgilanci
har sai sun komo zuwa gare su a lokacin sauki da lokacin cuta suka gaskata su a
sha'nin ilimin gaibi da labarin sama, hakika kuma ya tabbata daga Annabi Muhammad
an karbo daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce :Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (duk wanda ya zo ga mai duba
ko boka sa'nnan kuma ya gaskata shi cikin abin da ya fadi to hakika ya kafurce
da abin da aka saukar ga Muhammadu)
An kuma karbo daga Imrana dan Husaini
ya ce: Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce (baya
tare da mu duk mutumin da yake camfi ko ake mishi camfi kokuma ya ke bokanci ko
ake mishi bokanci ko ya ke sihiri ko ake mishi sihiri).
Lallai shaidanu kayan hajansu shi ne
karya da kirkira kage Allah Madaukakin sarki ya ce (shin
bazan baku labari ba bisa ga wanda shaidanu ke sauka a gare shi , suna sauka ne
a bisa dukkan mai yawan karya ko mai kage mai zunubi , su shaidanu suna jefa
saurara daga mala'iku ga bokaye yawancin su makaryata ne).
An karbo daga A'isha Allah ya kara
yarda a gare ta ta ce: wasu mutane sun tambayi Manzon Allah tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi game da masu bokanci sai ya ce :lallai su din nan
ba kome bane sai suka ce ya Manzon Allah lallai fa suna bamu labarin a wasu
lokutan abin da zai kasance kuma sai ya kasance gaskiya, sai Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : lallai mala'iku
suna sauka zuwa sama a wurin gajimare sai su ambaci abubuwanda za a hukunta a
sama sai shaidanu su sauraresu sai su dauki wannan sakon su kai shi zuwa
ga bokaye sai su kara musu karairayi akan
abin da suka ji guda dari daga garesu) . A wata riwayan (wancan kalma ce guda daya na gaskiya wanda aljani zai
fizgota sai sautin ya fada kunnen masoyansa kamar yanda kukan kaza yake
tabbatuwa a kunne sai ya . cakuda shi da karerayi sama da karya dari) Bukari da
muslim ne suka rawaito
Ya ku jama'n musulmi
Lallai shaidanun mutane da aljanu
abokan juna ne kuma makiya ne a gare ku Allah ya ce( sashinsu na wahayi zuwa ga
sashi suna masu kawata zance na rudi ) kuma hakika Allah ya musu alkawarin
narkon azaba gaba daya sai ya ce (A ranar da za a
tada su gaba daya ya tawagar aljanu gashi kun yawaita akan mutane sai masoyansu
na daga mutane suka ce : ya Ubangijinmu sashinmu sun ji dadi da sashi kuma
gashi mun kai lokacin da ka sanya mana sai ya ce ai wuta ne makoman ku kuna
masu dawwama a cikinta sai inda Allah ya so lallai Ubangijinka mai hikima ne
kuma masani)
Bayan haka: ya jama'r musulmai
lallai Allah shi ne wanda ya kebanta shi kadan shi da sanin gaibi duk wanda ya ikirarin
tarayya da Allah a cikin wani abu na wannan to hakika ya sanya wa Allah abokin
tarayya kuma ya yi karya ga Allah da Manzo lallai ku saurara duk wanda ya bar
da'a wa Allah zuwa da'a ga waninSa ya biye mishi cikin ala'marin addininsa to
hakika ya yi shirka ga Allah Madaukakin sarki, Allah Madaukakin sarki ya ce (lallai shaidanu suna yin wahayi zuwa ga masoyansu domin
su yi jayayya da ku, muddin kuka musu da'a to lallai ku din nan kuna cikin masu
shirka) ku yi riko da addininku da akidar ku domin ku kuna kan hanya mai
haske darenta kaman wuninta ne ba mai zamewa sai wanda ya ke halakakke.