Hudubar Farko
Ya ku musulmai!
Na daga cikin ni'imar Allah a gare mu da ya
shiryar da mu ga wannan Addini,ya kuma sanya mu musulmai: (Ku tuna ni'imar Allah a gare ku da Alkawari mai karfi da ya
yi da ku a yayin da kuka ce mun ji mun bi, ku ji tsoron Allah, lalle Allah
masani ne ga abin da ke cikin zukata.)
Ya ku
wadanda Allah ya musu ni'ima da kammala hajjinsu, ya wadanda aka musu baiwan
ayyukan da'a a lokutan alheri to ku gode wa Allah Mai tsarki ku tsayu a kan
lazimtar addininSa. Da shari'ar sa da nisatar saba mishi da kuma ketare iyakoki Allah madaukakin sarki
ya ce ;- (
Sai ka daidaita kamar yadda aka umurce ka kai da wadan da
suka tuba tare da kai
kuma ba masu kyatara haddi ba
lallai shi mai gani ne ga abin da kuke aikatawa )
(An karbo daga Abu Sufyan Dan
Abdallah As-sakafi Allah ya kara yarda a gare shi ya ce ;- Na ce ya manzon
Allah ka fada mini wani fadi a musulunci
wanda ba sai na tambayi wanin ka a bayan ka
ba sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce;- '' ka ce na yi imani da Allah sannan
ka daidaita ) muslim ne ya rawaito
Lallai
aikin musulmi a wannan rayuwa shi ne daidaituwa akan kadaita Allah mai tsarki da daukaka da dayanta bauta gaba daya a gare shi , shi
kadai adu'a ne, roko ne, fata ne , tsoro
ne da kuma kwadayi da firgici fadi da aiki
cikin da waje a bayyane da
boye Allah madaukakin sarki ya ce :- (ka ce lallai ne sallata
da ibada na da rayuwata da mutuwa
ta na Allah ne Ubangijin talikai babu abokin tarayya gare shi kuma da wancan
aka umarce ni kuma ni ne farkon masu
sallamawa )
Lallai ita ce daidaito wadda take sanya ka mai tsananin kauna ga mahaliccin ka tsarki
ya tabbata a gare shi tare da cikan
kankan da kai a gare shi wanda sha'anin sa ya buwaya da girmamawa,
lallai girmamawa ne wanda ya kunshi kadaita Allah wanda
yabon sa ya girmama sunayen sa sun tsarkaka da abin da ya kebanta da shi , mai tsarki na
daga rububiyya da uluhiyya da sunaye da siffofi Allah madaukakin sarki ya ce ;- (ku
bi abin da aka saukar zuwa gare ku daga
Ubangijin ku , kuma kada ku rinka bin wasu majibinta baicin sa)
(Kuma (ance mini) ka tsyar da
fuskarka ga addini kana karkata zuwa ga
gaskiya, kuma kada ka kasance daga masu shirka
kuma kada ka kirayi baicin Allah
abinda baya anfaninka kuma baya cutarka to idan ka aikata haka saannan lalle
kai a lokacin kana daga masu zalunci kuma idan Allah ya shafeka da wata cuta to
ba mai yaye maka ita sai shi kuma idan yana nufinka da wani alheri to ba mai mayarda
falalansa yana samun wanda yake so daga cikin bayinsa da shi kuma shi ne mai
gafara mai jin kai )
Manzon Allah tsira da amincin Allah
su tabbata a gare shi ya ce (ka kiyaye Allah sai
Allah ya kiyayeka ka kiyaye Allah za ka sameshi gaba gareka idan za ka roka ka
roki Allah idan za ka nemi taimako ka nemi taimakon Allah ) tirmizine ya
rawaito kuma ya ce hadisi hasan sahihi
Daidaituwa akan tafarki
mai tsiratar da bayi ita ce take sanya bawa ya zama mai kushuii gaba da girman
Allah ko wace girma ke kankanta gaba da
girmansa shi halitta duk yadda ya kai ga
masayi ko duk yadda ya kai ga martabansa ya daukaka to shi halattace ne kuma
abin raino ne wanda ake gudanar da shi abin mallaka. Allah Madaukakin Sarki ya
ce game da AnnabinSa: (Ka ce ba ni mallaka wa raina wani amfani kuma haka
ban tunkude wata cuta face abin da Allah ya so, kuma da na kasance ina sanin
gaibi da lalle ne da na yawaita daga alheri kuma cuta ba za ta shafe ni ba.ni
ban zama ba face mai gargadi kuma mai bayar da bishara ga mutane wadanda suke
yin imani).
Ya kai bawan Allah ka kwadaita daga
Allah kuma ka roke shi shi kadai ba shi da abokin tarayya, ya yaye cutarka ya
kawo ma amfani ya yaye ma bakin cikinka, Allah Madaukakin sarki ya ce : (Idan Allah ya shafe ka da wata cuta to babu mai kuranyewa
gare ta face shi, kuma idan ya shafe ka da wani alheri to shi ne akan komi mai
ikon yi ) kuma Allah mabuwayi mai girma ya ce : (ko wane ne yake karba wa mai bukata idan ya kira shi kuma ya sanya ku mamayan
kasa shin akwai wani abin bautawa tare da Allah?.kadan kwarai kuke yin tuna
lalle babbar manufa na
samuwarka -ya kai halitta a wannan rayuwa- shine don ka tsayu bisa tafarkin
Allah mikakke akan manhaji wanda yake na rayuwarka da kuma dabi'unka da
halayenka a cikin kai-komonka wahayin da aka saukar da shi yayi hukunci akanka
da kuma tarihin Annabi wanda aka turo amincin Allah su tabbata agare shi, Allah
madaukakin sarki ya ce: (kuma lalle wannan ne tafarkina yana madaidaici sai ku
bi shi kuma kada ku bi wasu hanyoyi su rarrabu da ku daga barin hanyata wannan
ne Allah yayi muku wasiyya da shi tsammaninku kuna yin takawa )
Ya bawan Allah ka tsayu bisa ga aiki da alkura'ni mai girma da
halaye kan sunnan shugaban annabawa da manzanni zahiri da badini kana mai
kuduri kuma kana aiki da shi kana mai hukunci da shi kuma kana mai nema ama
hukunci da shi, Allah Ubangiji tsarki da daukaka su tabbata a gare shi ya ce: (kuma ka bi abin da ake yin wahayinsa zuwa gareka kuma ka
yi hakuri har Allah ya yi hukunci kuma shi ne mafi alherin masu hukunci)
Allah Mai tsarki da daukaka ya ce :(saboda haka sai ka yi kira kuma ka daidaita kamar yadda
aka umarce ka kuma kada ka bi son zuciyarsu kuma ka ce na yi imani da abin da
Allah ya saukar na littafi)
Ya kai mumini ka lazimci kiyaye dokokin Allah kuma ka tsarkake aikinka gareshi
shi kadanshi ta hanyan nufatanshi da kuma nema, za ka kasance cikin walwala na har
abada da kuma aminci cikakke da rabauta mai girma duniya
da lahira za ka zama mafi tsarkakan mutane a rayuwa kuma za ka kasance mafi cikan ni'ima kuma za
ka zama mafi jin dadin rayuwa a cikin mutane da hali mafi dadi Allah madaukakin
sarki ya ce :(lalle ne wadanda suka ce Ubangijinmu
Allah ne sa'an nan suka daidaitu to babu wani tsoro a kansu kuma ba za su yi
bakin ciki ba)(wadannan 'yan Aljanna
ne suna madawwama a cikinta a kan sakamako ga abin da suka kasance suna
aikatawa )
Ya wanda ya sarayar da lokutan alheri ya
barnatawa kansa ta hanyar aikata zunubai da abubuwa masu halakarwa to ka koma
zuwa ga majibincinka Allah ka saurara zuwa ga abin da zai jefa maka fatan
alheri a cikin zuciyarka to ka kasa kunnuwarka tare da sauraro daga gareka
wanda zai ratsa cikin zuciyarka domin shi din nan kira ne daga wurin Ubangiji
wanda ke turo rahamarsa da kaunarsa ga bayinsa, lalle yekuwa ne daga gurin Ubangiji
Mai tausayi ga bayinsa duk yanda zunubi ya yi girma munanan laifuka suka
daukaka Allah madaukakin sarki yana cewa (ka ce (Allah
ya ce) ya ku bayina wadan da suka yi barna akan rayuwarsu kada ku yanke kauna
daga rahamar Allah, lalle Allah na gafarta zunubai gabadaya lalle shi, shi ne
mai gafara mai jin kai )
sannan ya kwadaitar da bayinSa zuwa
ga maida al'amari ga Allah da komawa gare shi kafin tserewan lokaci da sarayar
da zamani domin kar a fada cikin hasara da nadama game da sakacin yin da'a ga
Allah Mai rahama. Allah Madaukakin sarki yace : (kuma
ku mayarda al'mari zuwa ga ubangijinku kuma ku sallama masa a gabanin azaba ta
zo muku sa'nan kuwa ba za a taimake ku ba)
(kuma ku bi mafi kyaun
abin da aka saukar zuwa gare ku daga ubangijinku a gabanin azaba ta zo muku
bisa auke kuma ku ba ku sani ba)
Huduba ta Biyu
Ya ku bayin Allah ku tsayu kan da'a
ga Allah za ku rabauta, ku lazimci koyarwar Alkur'ani da sunna zaku samu
walwala, samun daukaka da shugabanci na ga lizimtar addinin Allah da bin sunnar
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, kuma kyakkyawan
karshe na ga tabbatar da tauhidi da tsoron Allah Mabuwayi abin girmamawa.
Allah Madaukakin sarki yace : (wadanda suka yi imani kuma basu gauraya imaninsu da
zalunci ba wadannan suna da aminci kuma sune shiryayyu)
Kuma kaskanci da walakanci da
tabewa da hasara na cikin sabawa Allah da munanan laifuka da sabawa umarni da
hani.
Allah Madaukakin sarki yace : (kuma wanda
ya sabawa Allah da ManzonSa kuma ya ketare iyakokinSa zai shigar da shi wuta
yana madawwami a cikinta kuma yana da wata azaba mai walakantarwa).