Lalle Dukkan Yabo da godiya sun tabbata ga Allah muna gode mishi kuma
muna neman taimakonsa kuma muna neman gafararsa , muna neman tsarin Allah daga
sharrin kawunan mu da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar da shi babu
mai batar da shi, kuma wanda Allah ya batar da shi babu mai shiryar da shi, Na
shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake ba shi da abokin
tarayya, shi ke da wanzuwa da kyakkyawan yabo, kaddartawa da hukuntawa na
hanunsa, yana gudanar da al'amura daga sama zuwa kasa, yana aikata abin da ya
so, ba za ku so ba sai abin da Allah ya halitta ya yarda.
kuma na shaida Annabi Muhammad
bawansa ne kuma manzonsa ne, ya isar da sako, ya sauke amana ya yi nasiha ga
al'uma, ya yi jahadi a tafarkin Allah cancancin jahadi har mutuwa ta zo mishi,
tsira da amincin Allah su tabbata agare shi da iyalansa da sahabbansa baki
daya, bayan haka:
To lalle mafi alherin zance shine maganar Allah, kuma mafi kyan
shiryarwa ita ce shiryarwar manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata
agare shi, kuma mafi sharrin al'amura sune fararrun ta, kuma dukkan bidi'a bata
ce kuma dukkan bata na wuta,
Ya ku bayin Allah ku ji tsoron Allah cikin abin da ya yi umarni, ku hanu
daga abin da ya hana ya tsawatar,kuna dukkan karami da babba abin rubutawa ne,
(ya ku wadanda suka yi imani ku ji tsoron Allah
cancancin tsoronsa kada ku mutu face kuna musulmai)
Ya ku jama'ar musulmai!
Allah ya kaddara abubuwan kaddarawa ya sanya musu lokaci, ya kuma kasa
musu arziki, ya rubuta ga kowanne rabonsa na rabauta ko tsiyace wa, da rabon
shi na ni'ima da yalwa da kuma tsanani da cuta, to duk wanda ya yarda zi samu
yarda wanda ya fusata yana da fushi, dukkan komai da hukuncin Allah ne da
kaddararsa.
Ya ku bayin Allah ! hakika Allah
ya rubuta arzikin bani-adam tun sunacikin mahaifa, idan mutum ya cika wata hudu
acikin mahaifiyarsa, sai Allah ya turo masa mala'ika da aka wakiltawa kula da
mahaifa sai ya busa masa rai da izinin Allah ya rubuta masa ajalinsa da aikinsa
da arziki kuma shakiyyi ne ko sa'idi,
An
karbo daga Abdullahi dan Mas’ud (R.A) yace manzon Allah (S.A.W) ya bamu labari,
shi ne mai gaskiya abin gaskatawa yace: lallai kowanne dayanku ana tara halittarsa
a cikin mahaifiyarsa, tsawon kwana arba’in yana maniyyi, sannan , ya canja ya
zama gudan jinni kwatankwacin
wannan, sannan ya juya ya zama tsoka kwatankwacin haka sannan, ya juya ya zama tsoka kwatankwacin haka, sai a aiko
mala’ika ya busa masa rai, a umarce shi da rubuta kalmomi guda hudu: A rubuta arzikinsa da ajalinsa da a ayyukansa da kuma dan wuta ne ko aljanna na rantse da wanda babu wani abin bautawa da gaskiya face shi lallai dayanku zai yi aiki irin na ‘yan Aljanna har ya zamanto baa bin da ke tsakaninsa da
Aljanna sai zira’i daya sai rubutun can ya rigaye shi, yayi aiki irin na ‘yan wuta, sai ya shige ta, lallai dayannku zai yi aiki irin na ‘yan wuta har abin da ke tsakaninsa da ita bai wuce zira’i daya ba, sai littafi ya rigaye shi sai yayi aiki irin aikin yan aljanna sai a shige ta) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
wannan, sannan ya juya ya zama tsoka kwatankwacin haka sannan, ya juya ya zama tsoka kwatankwacin haka, sai a aiko
mala’ika ya busa masa rai, a umarce shi da rubuta kalmomi guda hudu: A rubuta arzikinsa da ajalinsa da a ayyukansa da kuma dan wuta ne ko aljanna na rantse da wanda babu wani abin bautawa da gaskiya face shi lallai dayanku zai yi aiki irin na ‘yan Aljanna har ya zamanto baa bin da ke tsakaninsa da
Aljanna sai zira’i daya sai rubutun can ya rigaye shi, yayi aiki irin na ‘yan wuta, sai ya shige ta, lallai dayannku zai yi aiki irin na ‘yan wuta har abin da ke tsakaninsa da ita bai wuce zira’i daya ba, sai littafi ya rigaye shi sai yayi aiki irin aikin yan aljanna sai a shige ta) Bukhari da Muslim ne suka rawaito.
Arziki abu ne da an riga
an kasa shi, dukkan komai an yi shi ne da hukunci na Ubangiji da ajali sananne,to
ku dai ku nemi halal,ku nemi taimakon Allah,wajen neman arziki, ku kuma
kyautata zato ga Allah,domin mummunar zato abin zargi ne da bai da amfani,
Allah na ga inda bawansa ya kyautata
zato a gare shi, to ya kai bawan Allah ka rika kyakkawan fata,ka yarda da kason
da Allah ya diba maka, na hore ka da ka nesaci kwadayi da tsoro da handama, na
hore ka da sakaci, domin hakan wauta ne da almubazzaranci, idan
musiba ta same ka kada kace da da ba don kaza ba, sai dai kace Haka Allah ya
kaddara, kuma abin da ya so shi ya ke aikatawa.
Ya ku bayin Allah!
Allah shine mai bayarwa shi
ne Mai azurtawa, hannayensa biyu a shinfide suke yana ciyarwa yadda ya so,
taskokin sa ba su karewa, damarsa a cike take ciyarwa bata rage ta, mai yawan
kyauta ne dare da wuni.
"An karbo daga Abu-zarri (رضي الله عنه). Yace, Manzon Allah
tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace cikin abin da ya rawaito daga
Ubangijinsa Mai tsarki da daukaka ya ce : Ya ku bayi na ! lalle na haramta
zalunci wa kai na kuma na sanya shi haramun a tsakaninku, to kada ku yi zalunci,
Ya ku bayina! dukkaniku batattu ne, sai wanda na shiryar
da shi; ku nemi shiryarwata; in shiryar da ku. Ya ku bayina! dukkaninku
mayunwata ne sai wanda na ciyar da shi; sai ku nemi ciyarwata; in ciyar da ku.
Ya ku bayina! kowanenku tsirara ya ke; babu tufafi sai wanda na tufatar da shi;
sai ku nemi tufatarwata, in tufatar da ku. Ya ku bayina ! lallai kuna yin laifi
dare da rana, ni kuma ina gafarta zunubai gabadaya; sai ku nemi gafarata; in yi
muku gafara ya ku bayi na ba ku kai abin
da zaku cutar da ni ba balle ku iya cutar da ni, haka kuma ba ku kai abin da za
ku iya amfanar da ni ba balle ku amfanar da ni, ya ku bayi na da a ce na
farkonku da na karshenku da mutanenku da aljaninku zasu kasance da zuciyan mutum
guda mafi tsoron Allah a cikinku, to hakan ba zai kara komai a mulki na ba, ya
ku bayi na da ace na farkonku da na karshenku da mutanenku da aljaninku zasu
kasance da zuciyan mutum guda mafi fajirci a cikinku da hakan ba zai rage komai
ba a mulki na, , ya ku bayi na da a ce na farkonku da na karshenku da mutanenku
da aljaninku zasu tsaya a kan wata kasa guda suka roke ni na kuma bawa kowa
bukatansa da hakan ba zai rage wani abu na daga gare ni ba face kamar abin da
allura zai rage in an sa cikin kogi, ya ku bayi na lallai ayyukan ku ne nake kididdige
muku na cika muku, to wanda ya samu
alheri ya godewa Allah, wanda ya samu sabanin haka to kar ya zargi kowa sai
kansa) " Muslim ya ruwaito shi.
Ya ku bayin Allah !
Lalle Allah ya dauki nauyin azurtawa,sai yace : (Ba
wata dabba a cikin kasa face ga Allah arzikinta ya ke kuma ya san
matabbatarta da ma'azarta , duka suna cikin littafi bayyananne)
Yana azurta jariri a
cikin mahaifiyarsa da kifi a cikin ruwa, da macizai a cikin rami, Allah bai
taba halittar wasu halittu ba ya sarayar da su, da bawa zai gujewa arzikinsa da arzikin
ya riske shi, (Allah na yalwata arziki ga wanda
ya so daga cikin bayinsa kuma yakan kuntata wanda ya so).
Ya ku musulmai!
Allah kan jarrabi mutum
da arziki don ya kyautata ya bo ya gode, ya kan kuntata don jarabawa ba don ya manta ba ko
gazawa, to a nan sai ya lizimci hakuri.
Duk wanda talauci ta
sauka gare shi sai ya kai kuka ga wanin Allah to ba zai toshe mishi talaucin sa
ba, duk wanda ya nemi kame kai to Allah zai bashi kamewa, wanda ya nemi ya
wadatu Allah zai wadata shi, wanda ya nemi ya zama mahakurci Allah zai maishe
shi mahakurci,
To hakuri bisa talauci
da tsanani da tsadar rayuwa da jarabawa abu ne na wajibi a sharia kuma al'amari ne na larura na dole, Allah ya
zargi ga hakan sai ya ce : (To shi mutum idan
Ubangijinsa ya jarrabe shi ya karrama shi ya masa ni'ima sai yace Ubangiji na
ya karramani, to amma idan ya jarrabce shi ya ya kuntta mishi arzikinsa sai ya
ce Ubangiji na ya wulakanta ni)
Ya ku bayin Allah!
Tsoron Allah shine abu
mai riba mafi alheri ga bawa, shine
mafita daga duk wani kunci da sharri, (Duk wanda
ya ji tsoron Allah zai sanya mishi mafita kuma ya azurta shi daga ta inda bai
zato).
Tsoron Allah shi ne taskar
sammai da kasa,abin da ke gurin Allah ba a riskarsa da saba masa, (Kuma da lalle mutanen Alkaryu sun yi imani suka yi
takawa da mun bude Albarkoki a kansu daga sama da kasa to amma sai suka
karyata sai muka kama su da abin da suka kasance suna aikatawa)
Allah
ya sanya min albarka ni da ku a cikin Alkur'ani mai girma,kuma ya amfane ni da
ku da abin da ke cikinsa na ayoyi da ambato mai hikima, ina fadin abin da kuke
ji ina neman gafarar Allah mai girma, ga ni da ku daga dukkan zunubai, kuma ku
nemi gafarar sa lalle shi Mai gafara ne Mai jinkai.
Huduba ta biyu
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah,wanda ya halicci mutuwa da rayuwa don ya jarrabe ku wanene ya fi kyan aiki, ya kuma sanya
Albakiyatussalihatu ya zama mafi alheri a gurin Ubangijinka a lada da ku
kyakkyawan fata, tsira da amincin Allah su tabbata ga Annabinmu Muhammad wanda
ya fi tsarkin zance da aiki cikin halittu, da iyalansa da sahabbansa masu mutunci
da falala da tabiai da wadanda suka bi su da kyautatawa har zuwa ranar sakayya.
Ya ku bayin Allah !
Aiki mabudi ne na
kyakkyawan fata, mafi tsarkin abin nema shine sana'ar hanu, hannu mai mikawa ya
fi hannu mai karba, kame kai ya fi alheri bisa roko, wanda ya wadatu daga
waninsa ya daukaka kuma ya kare mutuncin kansa, Manzon Allah tsiran da
amincincin Allah su tabbata a gare shi yace: Na rantse
da wanda rai na ke hanunsa dayanku ya dauki igiyarsa ya je ya yi kirare ya dora
a bayansa ya fi alheri a gare shi da ya zo ga mutum ya roke shi, sawa'un ya ba
shi ko ya hana shi,) Bukhari ne ya rawaito.
Hakika Annabi Musa amincin Allah su tabbata a gare shi, ya kasance
yana kiwon dabobi ana biyansa, Annabin Allah Zakariyya ya kasance kafinta ne,
Annabin Allah Dauda amincin Allah ya tabbata a gare shi ya kasance yana ci daga
aikin hanunsa, Annabinmu Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi
ya kasance yana kiwon dabbobi na mutanen makka bisa wasu sulalla, ba wani
abinci da mutum zai ci da ya fi alheri bisa aikin hanunsa, Aiki daukaka ne
zaman banza kuma barna ne, (Shi, (Allah),
Yã sanya muku ƙasa hõrarriya, sai ku tafi cikin sãsanninta, kuma ku ci daga
arzikinSa, kuma zuwa gare shi ne tãshin yake)
(Ku tafi a doron kasa
ku nema daga falalar Allah)
Ku dogara gare shi, to duk wanda ya dogara a gare shi ya isan masa, (Kuma kada ku yi bakinciki game da abin
da ya tsere muku, kuma kada ku yi farinciki bisa abin da ya ba ku)
Ya ku musulmai!
Duniya mai karewa ne
kuma mai gushewa ce, lalle gidan lahira ita ce gidan rayuwa, ba rayuwa kamar
rayuwar lahira, Duniya jin dadi ne na rudi,mai saurin wucewa, mai saurin
sanjawa, ba ta tabbatuwa a hali guda, ta fi tsananin juyawa a kan ranaku da
dararraki, idan ta sauka a guri sai ta bata shi, in ta bayyana sai ta bada
tsoro,sau da yawa takan sa mutum dariya kuma ta sa shi kuka, ta faranta kuma ta
jiyar da ciwo, ta fiskanto ta kuma juya baya, ita ba wata aba ba ce sai
farinciki da bakinciki, jin dadi ne na holewa da kuma juyayi, kuma walwala ne
da annashwa,da bakinciki da bacin rai,kuma wargi ne da wasa, da kawa da
alfahari da tinkaho da yawa (Ku sani cewa rãyuwar dũniya wãsã ɗai ce da shagala da ƙawa
da alafahri a tsakãninku da gãsar wadãta ta dũkiya da ɗiya, kamar misãlin shũka
wadda yabanyarta ta bãyar da sha'awa ga manõma, sa'an nan ta ƙħƙashe, har ka
ganta tã zama rawaya sa'an nan ta kõma rauno. Kuma, alãmra akwai azãba mai
tsanani da gãfara daga Allah da yarda. Kuma rãyuwar dũniya ba ta zama ba fãce ɗan
jin dãɗin rũɗi kawai).
Mutum bai da wani abu cikinta sai
abin da ya gabatar ko ya ci ya karar, ko ya sanya tufafi har ya tsufar ya
rididdige, ko ya yi sadaka ya shude, to ka kasance a duniya kamar wani bako ko mai
ketare hanya, jin dadin rayuwar duniya dan kadan ne, lahira ta fi alheri ga
wanda ya ji tsoron Allah, kuma ita ta fi alheri da wanzuwa, ka guji duniya
Allah zai so ka, ka guji abin hanun mutane, sai mutane su so ka.
Bayan haka ya jama'ar musulmai!
To lalle duniya za ta kaura tana mai juya baya,lalle kuma lahira za ta
fiskanto, kowacce na da 'ya'ya, to ku kasance daga 'ya'yan lahira, kar ku
kasance daga yaran duniya, to lalle yau aiki ne ba hisabi, gobe kuma hisabi ne
ba aiki.
To ka gaggauto zuwa ga Aljannar Adni,domin ita ce masaukanka na farko
cikinta akwai shemomi,
ya kai mai saida wannan da raha kana mai gaggawa,
kai ka ce baka sani bane
aaha zaka sani.
To in baka sani ba ne to wannan musiba ce.
In ka kasance kana sane to musibar ta fi girma.