Hudubar Masallacin
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi 11-1-1440AH na sheikh Ali Abdurrahman
Al-Huzaifi
HUDUBAR FARKO
DA SUNAN ALLA MAI RAHAMA MAI JIN KAI
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah mabuwayi mai yawan kyauta mai gafaran zunubai mai karban
tuba , mai tsananin ukuba ma'abocin
yalwa , ba abin bautawa da gaskiya sai shi
komawa na gare shi ina kyautata yabo ga Ubangijina kuma ina gode
mishi , ina tuba zuwa gare shi kuma ina
neman gafarar sa, na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kadai yake
ba shi da abokin tarayya madaukaki mai girma ,
kuma ina shaidawa Annabin mu Muhammadu bawan sa ne kuma Manzon sa ne ,
mai albishir kuma mai gargadi , ya Allah ka yi dadin tsira da aminci da albarka bisa ga bawan ka kuma Manzon ka Muhammad da iyalan shi da sahabban shi wanda suka tsere zuwa ga dukkan falala da alheri .
BAYAN HAKA: - Ku ji tsoron
Allah ta hanyar bin umarninsa da nisantar
abin da ya hana ya tsawatar, ya ku bayin Allah;
ku yi aiki irin ayuka na kwarai domin gyara lahiran ku kada ku bata ayukan ku sai ku yi hasara wa
kanku Allah madaukakin sarki ya ce ( Ka ce ku yi aiki Allah zai ga ayukan ku da Manzon sa da
muminai sannan a maice ku zuwa ga masanin gaibi da shahada , sai ya baku
labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa )
Allah madaukakin sarki ya ce : (Ya ku
wadan da suka yi imani ku yi da'a ga Allah ku yi da'a ga Manzo kar ku bata ayukan ku ).
Kuma Allah madaukakin
sarki ya ce : (Lallai hasararru su ne wadanda suka yi hasarar kawunan su
da iyalan su , ranar alkiyama ,
wannan shi ne hasara mabayyani )
Ku gyara duniyan ku ta
hanyar neman halal da ciyar da shi cikin
kofofin alheri na wajibi da mustahabbi
da kuma halal , ku sanya wannan
duniya din ta zama guzuri a gare ku zuwa
gidan ni'ima kada kawa ta duniya ta rude ku ko ta
fitine ku game da lahira , ka yi aiki ya kai Musulmi domin gyara duniyar ka, ka yi
aiki kuma domin gyara lahirar ka , ya zo a hadisi ba mafi alherin ku shi ne wanda ya bar
lahirar sa don duniyar sa ba , ko kuma
wanda yabar duniyar sa don lahirar sa ba
, An karbo daga Mustaurid dan Sadad Allah ya kara yarda a gare shi ya ce
: ( Mun kasance a wurin Annabi tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi muna tuna
duniya da lahira , wasun su suka ce duniya kawai guzuri ne zuwa ga lahira , acikin
ta akwai aiki akwai salla , akwai zakka
, wasu daga cikin su kuma sai suka ce lahira a cikin ta akwai aljanna suka fadi abin da Allah ya so su fada, sai
Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce :-Misalin
duniya in an kwatanta da lahira kamar dayanku ne ya tafi kogi ya sa yatsarsa ciki ya fitar to
ruwan da yatsar ta debon shine duniya,) Hakim ya rawaito a cikin Al Mustadrak,
kuma Hakim ya rawaito daga Sa'ad dan Darik daga baban shi daga Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce:
(Madalla da gidan duniya ga wanda ya yi guzurin lahirar sa daga gare
ta har ya yardar da Ubangijin shi , tir
ga wanda ta kange shi daga lahirar sa ta
gajarta mishi samun yardan Ubangijin shi ).
Hasanul-Basari
Allah ya mishi rahama ya ce : - ( Madalla da gidan duniya ga mumini sabo da ya yi aiki dan kadan a cikin ta ya
karbi guzurin sa daga gare ta zuwa
aljanna, tir da gidan
da ta kasance ga munafiki da kafiri sabo da ya sarayar da dararrakin sa
sai guzurin sa ta kasance a cikin ta zuwa wuta Ahmad ne ya rawaito a cikin
littafin zuhud .
Kowa ya san dahir cewa shi din nan mai kaura ne
daga wannan gidan kuma ya bar abin da Allah ya bashi anan duniya
a bayan shi ba abin da zai kasance tare
da shi sai aikin shi, in alheri ya yi ya
ga alherin sa in kuma sharri ya yi ya ga sharrin sa to idan har ya kasance halin ko wani daya zai
kai ne zuwa ga wannan gayan kuma zai kai ga wannan makomar , to ya wajaba a gare shi da ya kaddamar da
aiki mafi daraja da zai iya yi ga ubangijin shi
na daga cikin ayuka na kwarai ba wata
wasila tsakanin bawa da Ubangijin shi sai da wannan Allah madaukakin sarki ya ce :- ( Ba wai
dukiyan ku ne ba ko 'ya'yan ku ne suke
kusantar da ku zuwa gare mu kusantarwa ba
face wanda ya yi imani ya yi aiki na kwarai to wadancannin ka suna
da sakayya na ribi sabo da abin da suka
aikata alhali kuma suna cikin benayen
aljanna a cikin aminci ).
Babban damuwar ka ya kai musulmi shi ne ka
samu rabauta da sha daga tabkin Annabi
shugaban 'yan Adam tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi , (To yaya za ka cimma
wannan manufan? shi ne farkon abin sha
na 'yan aljanna, to duk wanda Allah ya
datar da shi ya mishi baiwan sha daga wannan tafkin to babu tsoro a gare shi bayan haka , wanda ya
kasance daga cikin wadan da za su zo ga Annabi
su
sha a tafkin Allah zai saukake musu fitintinun kafin
haka.
kuma imani
da tafikin imani ne da ranar lahira , wanda bai yi imani da tafkin ba bai da imani
sabo da rukunnan imani ba a rarrabewa tsakanin su to duk wanda ya
bar wani rukuni daga cikin rukunnan imani hakika ya kafurce da su gaba daya .
Shi Tafki wani kyauta ne daga Allah zuwa
ga Annabi sa Muhammad tsira da amincin
Allah su tabbata a gare shi, al'umar
sa za su sha daga gare shi a kasar da za a tattara al'uma a wurin hisabi ranar
alkiyama a wunin da mikidarin sa ya kai shekara dubu hamsin ga
kafura Allah zai gajarta shi ga
muminai zai lullube mutane
a wannan ranar awurin
hisabi tare da bakin ciki
wanda ba za su iyada shi ba ba don Allah ya bawa jikkunan su karfin
juriya ba da wanzuwa ba da duk sun mutu gaba daya kuma zai jarrabe su da kishi mai tsanani wanda ke kona hanta a gun tsayawa na hisabi zai jefa kishi mai tsanani a cikin ciki irin
kishin da ba su taba yin irin shi ba ,
Allah zai karrama Annabin sa Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata
a gare shi da tafki domin al'uman shi su sha daga gare shi , shi kuma Manzon
Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana tsaye a gindin tafkin yana dubi zuwa ga al'umarsa yana jin dadin haka, jin dadi mai girma yana kiran al'umar sa don su sha ,
fadin tafkin da yalwan sa , hadisai masu dumbin yawa sun zo wurin bayanin sifar
ruwan da yalwan shi haka kuma alkur'ani ya zo da ambaton sa a
cikin suratul kausar kuma ko wani
Annabi na da tafki , an karbo daga Samarata Allah ya kara yarda a gare shi (
daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce lallai Annabawa za su yi tinkaho a
tsakanin su ko wane ne ya fi yawan
mabiya a cikin al'uman sa to ina
fatan ya kasance a wannan ranar na fi su duka
mazowa sha kuma ko wani mutum a cikin
su a wannan ranar yana tsaye a
kan tafkin cikakke yana tare da sanda yana kiran duk wanda ya sani a cikin al'umar sa kuma ko wace al'uma na da alama wanda Annabin su zai gane su da ita). Tirmizi da Dabarani suka
rawaito.
Kuma tafkin Annabin mu shi ya fi girma kuma
yafi dadi kamar dai shari'arsa An karbo
daga Abu Huraira Allah ya kara yarda a gare shi ya ce : - daga Annabi tsira da
amincin Allah su tabbata a gare shi ya ce : ( Lallai
tafki na ya fi nisan daga garin Aila zuwa Adan , kuma lallai ya fi nono fari ya fi zuma zaki
ya fi kankara sanyi, kuma adadin kwanukan shan shi ya fi yawan taurari
) Muslim ne ya rawaito, a wata ruwaya da ba na muslim ba ya
fi turaren almiski kamshi.
An karbo daga Abu Zarri Allah ya kara yarda a gare shi ya ce:- Daga Annabi tsira da amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce :- (Na rantse da wanda rai na yake hanun shi ,;
kwanukan shan sa sun fi adadin taurarin da ke sama da kuma
manyan taurarin ta na sama a cikin dare mai duhu, kwanon aljanna kuma wanda ya sha daga gare shi ba zai ji kishi ba
har abada yana tsatssagowa daga gare shi indororo guda biyu na aljanna ), Ahmad ne ya rawaito da Muslim da nasa'i
An karbo daga Abu Umama
Allah ya kara yarda a gare shi daga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi ya ce (Tabki na ya kai
kwatankwacin Adan da Amman, ya fi girma kwarai akwai magudanar ruwa guda biyu :na azurfa da zinari,
ruwansa ya fi nono fari, ya fi zaki akan zuma, ya fi turaren Al miski
kamshi,duk wanda ya sha daga shi ba zai ji kishi bayan haka, fiskarsa ba zata
bakanta ba har abada,) Ahmad da Ibnu Maja da Ibnu Hibban.
An karbo daga zaid
bin khalid Allah kara yarda a gare shi, daga Annabi tsira da Amincin Allah su
tabbata a gare shi ya ce: Shin ko kun san Alkausar? Wani kogi ne da Ubangiji na
ya ba ni a Aljanna, yana da alheri mai yawa a cikin shi, Al'uma ta zata sha
daga gare shi ranar alkiyama, kwanukan shan sa kamar adadin taurari, zaa fizge
bawa daga gare su sai na ce : ya
Ubangiji na ai ya na cikin Al'uma ta sai ace : Ai baka san me ya farar a
bayanka ba,) Ahmad ne da Muslim da Abu Da'uda,.
Tafkin kasa ne mai fadi, Allah zai cika shi da ruwan Alkausara,
yana kwarara a cikin sa Indororo guda biyu na zinari da azurfa na daga kogin Alkausara, wannan tafkin bai
raguwa, kuma kowani mumini da muna zasu sha daga shi, bisa ga kishi mai
tsananin gaske, to bayan an sha ba za a ji kishi ba har abada, masu zuwa ga
Annabi a tafkin su ne masu bin sunnarsa tsira da amincin Allah su tabbata a
gare shi, da kuma masu nesatan manyan zunubai, Allah Madaukakin sarki yace : In
kun nesaci manyan zunubai da muka hane
ku, zamu kankare muku zunubanku kuma mu shigar da ku mashiga mai girma
(Aljanna).
Tare da bin sunnar
Annabi suna kira zuwa ga Allah bisa basira, Allah Madaukakin sarki ya ce :
(ka ce wannan ne hanya ta ina kira zuwa ga Allah bisa basira ni da wanda ya bi
ni, tsarki ya tabbata ga Allah kuma ni ba na cikin masu shirka.) sai su kira zuwa ga shariar Annabi Muhammad,su
nesaci bidia da fararrun abubuwa a
addini, da abubuwan da sharia ta ki na munkari, kuma suna lazimtar Ikhlasi
mai kore riya da neman aji, da nau'uka na shirka, Allah
Madaukakin sarki ya ce : (Da sunan Allah mai rahama mai jinkai, lallai mun
baka Alkausar, ka yi sallah don Ubangika kuma ka yi suka,) Assura
Allah ya sa min
Albarka ni da ku a alkur'ani mai girma.
Dukkan yabo da godiya
sun tabbata ga Allah Ma'abocin girma da karramawa,da mulki da ba a samun irin
shi, da buwaya wacce babu zalunci,ina kyautata yabo ga Ubangiji na kuma ina
gode mishi bisa ni'imtarwa masu yawa,na shaida ba abin bautawa da gaskiya sai
Allah, shi kadai ya ke ba shi da abokin tarayya, Mai mulki kuma tsarkakakke,
kubutacce daga aibi, na shaida cewa Annabinmu kuma shugabanmu Muhammad bawansa
ne kuma manzonsa ne,kuma Manzonsa
ne,tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da iyalansa da
sahabbansa masu daraja, bayan haka ku ji tsoron Allah cancancin tsoronsa, ku yi
riko da igiya mai karfi na musulunci,
Ya ku bayin Allah! Abin
mamaki da falala irin na wanda Allah ya mar falalar zuwa tabkin Annabi na
Alkausara ya sha daga gare shi, ba zai ji kishi ba har abada, kuma abin mamaki
da girman hasarar wanda aka hana shi sha
kuma aka kore shi daga gare shi, Ubangijinka bai zaluntar kowa,.
Ya ku Musulmai! Na daga
cikin abubuwan da ke hana isa a sha daga wannan tabkin akwai kirkiran bidi'o'i da
farar da abubuwa cikin addini, da kuma yin saddu ga musulunci ta hanyar fadi ko
aiki, kamar yadda ya zo a hadisan da aka rawaito kan sababin koran wasu daga
cikin wannan al'uma.cikin wadannan hadisan akwai fadin : (Ba ka san me suka
farar ba a bayanka,sai manzon Allah ya ce : Nesa daga rahamar Allah ga duk
wanda ya canja a baya na, )>
na daga cikin abin da
ke hana sha daga tabkin alkausara akwai
manyan zunubai, domin suna kazanta zukata, haka nan riya da son a sani ko son a
ji na daga cikin abubuwan da ke hana samun isa ga tabkin alkausara, haka
hakkokin wasu da aka zalunta na cikin manyan abubuwan da ke hana samun sha daga
tabkin, kuma sakayyar ta yi daidai da aikin ga wanda ya yi lura, domin wanda ya
bi shariar Annabi Muhammad a nan duniya ya kuma bi koyarwarsa to zai sha daga
tabkinsa, wanda kuma ya sanja ya yi bidia sai ahana shi sabo da saddu da ya yi
ga Allah.
Lalle Allah da
mal'ikunsa suna salati ga Annabi ya ku wadanda suka yi imani ku yi salati a
gare shi da aminci tabbatacce.